Dakarun ‘Operation Hadin Kai’ (Arewa maso Gabas) sun kashe ‘yan ta’adda 18 a wasu hare-haren haɗin gwiwa da aka kai a yankin iyakar jihohin Borno da Yobe.
Jami’in Yaɗa Labarai na rundunar, Laftanar Kanal Sani Uba, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da aka rabawa manema labarai ranar Laraba.
Ya ce an kashe ‘yan ta’addan ne yayin hare-haren farmaki da aka gudanar ƙarƙashin ‘Operation Desert Sanity V’ a sansanonin da aka gano a Mar, Subdu, Yaro Lawanti da Yaro Shuwari, da kuma wasu yankuna da ke kusa da dajin Bulabulin da yankin Kamadogu Yobe.
A cewarsa, dakarun Shiyya 2 ne suka gudanar da aikin tare da haɗin gwiwar rundunar jami’an tsaro ta farin kaya, tare da tallafin hare-haren sama daga rundunar sojin sama.
Uba ya ce rundunar sojin saman ta taka muhimmiyar rawa wajen samar da bayanan sirri, sa ido da bincike (ISR) ba tare da yankewa ba, wanda hakan ya taimaka wajen gano sansanonin maharan, inda sojoji daga ƙasa suka farmaki wuraren.















Discussion about this post