Tanzania ta tabbatar da shirinta na jan hankalin adadi mai yawa na Sinawa masu yawon bude ido, yayin da kasashen Afrika ke inganta kokarinsu na cin gajiyar babbar kasuwar tafiye-tafiye ta duniya.
Wata sanarwa da hukumar kula da yawon bude ido ta Tanzania (TTB) ta fitar jiya Laraba ta ce an yanke shawarar ce yayin wata tattaunawa ta manyan jami’ai mai taken “Yanayin Tafiye-Tafiye a Wajen Kasar Sin da Wuraren Zuwa a Nahiyar Afrika,” wanda ya gudana yayin taron kasuwar tafiye- tafiye ta duniya ta 2026, a birnin Cape Town na Afrika ta Kudu. Taron ya hada masu ruwa da tsaki na masana’antar yawon bude ido, domin lalubo dabarun mayar da nahiyar Afrika wuri mai jan hankalin Sinawa matafiya.
Ephraim Mafuru, darakta janar na hukumar TTB da ya wakilci Tanzania a taron, ya ce kasarsa ta shirya sosai wajen jan hankalin Sinawa kuma tana da fahimta sosai kan abubuwan da suka fi so da abubuwan da suke sa ran gani.
Masu tattaunawa yayin taron sun nanata cewa, dole ne kasashen Afrika su inganta ababen more rayuwa da karfafa dabarun kasuwanci da tsara harkokin yawon bude ido da za su dace da abun da Sinawa ke muradi. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)














Discussion about this post