An kammala taron ministocin cinikayya na kungiyar hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya ta kasashen Asia da tekun Pasifik (APEC) a jiya Asabar a birnin Suzhou na kasar Sin, inda ya nemi a cimma matsaya ta bai daya, domin dukkan bangarori su shiga a dama da su cikin hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya.
Ministan kula da cinikayya na kasar Sin Wang Wentao wanda ya bayyana hakan, ya kuma yi karin bayani kan sakamakon taron, yana mai cewa, ya nanata goyon baya mai karfi ga burin yankin ciniki cikin ‘yanci na Asia da tekun Pasifik mai dogon zango, inda dukkan bangarori suka yi alkawarin inganta dunkulewar tattalin arzikin yankin.
Ya ce, taron ya kuma aike da sako na hadin gwiwa kan bukatar yi wa hukumar kula da cinikayya ta duniya (WTO) garambawul, tare da samar da wata taswirar raya bangaren bayar da hidimomi cikin shekaru 10 masu zuwa.
Ya ce, bisa la’akari da kalubalen da yanayin duniya ke fuskanta, sakamakon taron abu ne mai muhimmanci sosai, yana cewa, Sin za ta ci gaba da hada hannu da sauran kasashe wajen aiwatar da muhimman matsayar da aka cimma yayin taron da kyautata samar da karin sakamako da cimma matsaya daya da bayar da kyawawan gudunmuwa ga taron shugabannin kasashen kungiyar ta APEC da za a yi nan gaba a bana. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post