ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

by Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago

Cibiyar Binciken Noma ta (Institute for Agricultural Research), tare da haɗin gwiwar African Agricultural Technology Foundation da shirin BMSS, sun samu nasarar fara horarwar manoma kafin kakar noma ta shekarar 2026 domin ƙarfafa noman masara da inganta ɗorewar ayyukan noma a faɗin Nijeriya.

Shirin horarwar na kwanaki biyu, wanda ya fara ranar Talata, 12 ga Mayun 2026, ya haɗa mahalarta daga jihohi daban-daban na ƙasar, ciki har da manoma, masu bincike, jami’an yaɗa harkokin noma da ƙwararrun masu fasaha, waɗanda suka duƙufa wajen inganta yawan amfanin masara ta hanyar amfani da dabarun noma na zamani da kuma hanyoyin yaƙi da ƙwari masu lalata amfanin gona.

An fara shirin da addu’o’i da gabatar da kai, lamarin da ya bai wa mahalarta damar mu’amala, musayar ƙwarewa da kuma ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin masu ruwa da tsaki a harkar noman masara.

ADVERTISEMENT

A jawabin maraba, babban mai bincike na shirin BMSS, Farfesa Rabiu S. Adamu, ya nuna godiya bisa yadda mahalarta suka amsa gayyata duk da ɗan ƙanƙanin lokacin sanarwa kafin fara shirin.

Ya jaddada cewa an tsara horarwar ne domin ƙarfafa noman masara, musamman a Arewacin Nijeriya, ta hanyar ingantattun dabarun noma, kula da ƙwari da cututtukan amfanin gona yadda ya kamata, da kuma amfani da ingantattun hanyoyin kula da Tela Maize.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Babban Daraktan Institute for Agricultural Research, Farfesa Ado Yusuf, wanda Mataimakin Daraktan Bincike, Farfesa L. J. Bamaiyi ya wakilta, ya bayyana horarwar a matsayin wacce ta zo a kan lokaci kuma mai muhimmanci, musamman yayin da manoma da masu ruwa da tsaki a harkar noma ke shirin tunkarar kakar noman shekarar 2026.

Ya ƙarfafa mahalarta taron da su shiga cikin zaman horarwar sosai tare da amfani da damar wajen samun ilimi na aikace da na kimiyya wanda zai taimaka wajen inganta dasa amfanin gona da yawan amfanin da ake samu.

Taron ya ƙunshi gabatar da muhimman muƙaloli daga fitattun masana kimiyya da ƙwararru a fannin noman masara da kula da amfanin gona.

Farfesa Rabiu S. Adamu ya gabatar da muƙala mai taken “Kula da Muhimman Ƙwari da Cututtukan Masara,” inda aka wayar da kan mahalarta kan yadda ake gano manyan ƙwari da cututtukan da ke shafar noman masara, hanyoyin kariya da yadda ake magance su.

Wata muhimmiyar muƙala da Farfesa M. M. Abdulmalik ya gabatar mai taken “Fari da Tasirinsa ga Yawan Amfanin Masara.”

Muƙalar ta mayar da hankali ne kan yadda fari ke shafar bunƙasar masara da kuma hanyoyin da manoma za su iya amfani da su wajen rage asarar amfanin gona sakamakon sauyin yanayi.

Haka kuma mahalarta sun sami ƙarin haske kan yadda ake samar da irin masara mai haɗaɗɗen jinsi (hybrid) ta hanyar gabatarwar Dakta H. Abubakar mai taken “Samar da Irin Masara na Hybrid.”

Muƙalar fasaha ta ƙarshe ta ranar kuwa Dakta M. S. Usman ne ya gabatar mai taken “Kula da Juriyar Ƙwari a Tsarin Kula da Tela Maize.”

Zaman ya jaddada muhimmancin amfani da ingantattun hanyoyin kula da Tela Maize, sa ido kan yawaitar ƙwari da kuma dabarun ɗorewar yaƙi da su domin tabbatar da ingancin fasahar masarar da ke da juriyar ƙwari.

Ɗaya daga cikin abubuwan da suka fi ɗaukar hankali a horarwar su ne zaman tambayoyi da amsoshi mai cike da mu’amala, inda mahalarta suka gabatar da tambayoyi masu alaƙa da aikace-aikace tare da bayyana abubuwan da suka fuskanta a gonaki.

Cibiyar IAR ta jaddada aniyarta na ci gaba da ƙarfafa samar da amfanin gona ta hanyar bincike, ƙirƙire-ƙirƙire, gina ƙwarewa da kuma yaɗa fasahohin noma masu ɗorewa.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Soyayyar Liverpool Ba Za Ta Taɓa Gushewa Daga Zuciyata Ba – Salah

Soyayyar Liverpool Ba Za Ta Taɓa Gushewa Daga Zuciyata Ba – Salah

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026
'Yan Bindiga

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.