Tawaga ta 27 ta jami’an lafiya ta kasar Sin mai aiki a Saliyo, ta bayar da tallafin magungunan cututtuka masu haifar da zubar jini ga ma’aikatar kiwon lafiya da tsaftar muhalli ta kasar Saliyo.
Tawagar ta mika tallafin ne a ranar Juma’a a birnin Freetown fadar mulkin kasar ta Saliyo, a wani kokari na karfafa ikon kasar na shawo kan cutar Lassa da sauran cututtuka masu yaduwa.
Tallafin ya kunshi alluran Ribavirin 18,000, allurar da ake amfani da ita wajen magance cututtukan zazzabi mai haifar da zubar jini ciki har da zazzabin Lassa.
Tawagar jami’an lafiyar ta kasar Sin, ta ce ta samar da tallafin ne biyowa bayan bukatar gaggawa da ta bayyana, sakamakon karancin magunguna da kasar ta Saliyo ke fuskanta.Da yake tsokaci yayin bikin karbar tallafin, babban shugaban hukumar kiwon lafiya da tsaftar muhalli ta Saliyo Sartie Kenneh, ya ce samar da juriya ta fuskar magunguna, muhimmin mataki ne na shawo kan cututtukan zazzabi masu yaduwa.
Ya kuma godewa gwamnatin kasar Sin, da tawagar jami’an lafiyar kasar bisa ci gaba da tallafawa Saliyo, yana mai bayyana hakan a matsayin mataki da ya zo a kan gaba, wanda kuma ake matukar bukatarsa.
Bugu da kari, mista Kenneh ya ce tsarin kiwon lafiya na Saliyo ya samu karin juriya, daga bukatun kiwon lafiya na gaggawa da ya fuskanta a baya, ya kuma jaddada cewa tallafin da Sin ke ci gaba da samarwa, ya zamo muhimmin jigo na karfafa ikon Saliyo, a fannin kandagarki da tunkarar yaki da cututtuka. (Mai fassara: Saminu Alhassan)














