ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

by Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago

Jami’an Hukumar Tsaron ta Nijeriya ta (NSCDC) reshen Jihar Kano sun kama wasu mutum 10 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban da suka haɗa da lalata kayayyakin gwamnati, sata, haɗa baki wajen aikata laifi, shiga haramtacciyar hanya da kuma karɓar kayan sata.

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, SC Ibrahim Abdullahi, ne ya fitar ranar Laraba, ya ce an kama waɗanda ake zargin a wurare daban-daban a Jihar.

Sanarwar ta ce wuraren da aka kama su sun haɗa da Gwarmai a Ƙaramar Hukumar Ghari, yankin masana’antu na Challawa, Unguwar Rimi da Waratallawa duk a Ƙaramar Hukumar Kumbotso ta Jihar Kano.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ƙara da cewa: “Rundunar NSCDC ta Jihar Kano ta samu nasarar cafke wasu gungun masu aikata laifuka 10 da ake zargi da lalata kayayyakin gwamnati, sata, haɗa baki wajen aikata laifi, shiga ba bisa ƙa’ida ba da kuma karɓar kayan sata.”

An kuma bayyana cewa kwamandan hukumar na Jihar, Commandant Mohammed Hassan Agalama IION, ya gabatar da waɗanda ake zargin a hedikwatar rundunar ranar Talata.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

Kayayyakin da aka ƙwato daga hannunsu sun haɗa da mita 200 na wayoyin aluminium, wayoyin hannu, wayoyin copper, power bank da kuma muggan makamai kamar wuƙaƙe, adda, takobi da almakashi da sauransu.

Sanarwar ta ce an kammala bincike kuma nan ba da jimawa ba za a gurfanar da waɗanda ake zargin a kotu domin fuskantar hukunci.

Kwamandan ya sake jaddada ƙudirin hukumar wajen kare muhimman kadarorin ƙasa da kayayyakin more rayuwa, tare da nuna rashin amincewa da duk wani nau’in aikata laifi. Ya kuma roƙi al’ummar Jihar Kano da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro bayanai domin magance matsalolin tsaro.

A wani labarin kuma, rundunar NSCDC ta Jihar Kwara ta kama wasu mutane uku bisa zargin haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba da kuma safarar ma’adanai a birnin Ilorin.

Waɗanda aka kama sun haɗa da Musa Abdullahi mai shekara 45, Aliyu Ibrahim mai shekara 20 da Ishaƙ Ibrahim mai shekara 51. An ce an kama su ne a wani samame na sirri da jami’an sashen ma’adanai da ƙarafa na rundunar suka gudanar da daddare.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi
Tsaro

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Hakimin Gundumar Gwande A Jihar Filato

June 19, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Manyan Labarai

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
Next Post
Yankin Hong Kong Na Kasar Sin Ya Zama Cibiyar Kula Da Jarin Ketare Mafi Girma A Duniya

Yankin Hong Kong Na Kasar Sin Ya Zama Cibiyar Kula Da Jarin Ketare Mafi Girma A Duniya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026
Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.