ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano

by Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago

Jami’an Hukumar Tsaron ta Nijeriya ta (NSCDC) reshen Jihar Kano sun kama wasu mutum 10 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban da suka haɗa da lalata kayayyakin gwamnati, sata, haɗa baki wajen aikata laifi, shiga haramtacciyar hanya da kuma karɓar kayan sata.

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, SC Ibrahim Abdullahi, ne ya fitar ranar Laraba, ya ce an kama waɗanda ake zargin a wurare daban-daban a Jihar.

Sanarwar ta ce wuraren da aka kama su sun haɗa da Gwarmai a Ƙaramar Hukumar Ghari, yankin masana’antu na Challawa, Unguwar Rimi da Waratallawa duk a Ƙaramar Hukumar Kumbotso ta Jihar Kano.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ƙara da cewa: “Rundunar NSCDC ta Jihar Kano ta samu nasarar cafke wasu gungun masu aikata laifuka 10 da ake zargi da lalata kayayyakin gwamnati, sata, haɗa baki wajen aikata laifi, shiga ba bisa ƙa’ida ba da kuma karɓar kayan sata.”

An kuma bayyana cewa kwamandan hukumar na Jihar, Commandant Mohammed Hassan Agalama IION, ya gabatar da waɗanda ake zargin a hedikwatar rundunar ranar Talata.

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Kayayyakin da aka ƙwato daga hannunsu sun haɗa da mita 200 na wayoyin aluminium, wayoyin hannu, wayoyin copper, power bank da kuma muggan makamai kamar wuƙaƙe, adda, takobi da almakashi da sauransu.

Sanarwar ta ce an kammala bincike kuma nan ba da jimawa ba za a gurfanar da waɗanda ake zargin a kotu domin fuskantar hukunci.

Kwamandan ya sake jaddada ƙudirin hukumar wajen kare muhimman kadarorin ƙasa da kayayyakin more rayuwa, tare da nuna rashin amincewa da duk wani nau’in aikata laifi. Ya kuma roƙi al’ummar Jihar Kano da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro bayanai domin magance matsalolin tsaro.

A wani labarin kuma, rundunar NSCDC ta Jihar Kwara ta kama wasu mutane uku bisa zargin haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba da kuma safarar ma’adanai a birnin Ilorin.

Waɗanda aka kama sun haɗa da Musa Abdullahi mai shekara 45, Aliyu Ibrahim mai shekara 20 da Ishaƙ Ibrahim mai shekara 51. An ce an kama su ne a wani samame na sirri da jami’an sashen ma’adanai da ƙarafa na rundunar suka gudanar da daddare.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tsaro

NDLEA Ta Cafke Ƴar Shekara 67 Da Hodar Iblis Da Aka Ɓoye A Cikin Ayaba

July 11, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara
Tsaro

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Next Post
Yankin Hong Kong Na Kasar Sin Ya Zama Cibiyar Kula Da Jarin Ketare Mafi Girma A Duniya

Yankin Hong Kong Na Kasar Sin Ya Zama Cibiyar Kula Da Jarin Ketare Mafi Girma A Duniya

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.