Rukuni na 27 na tawagar likitocin kasar Sin da ke kasar Saliyo ya bayar da gudummawar kayayyakin kiwon lafiya ga asibitin sada zumuntar Saliyo da Sin, inda hakan ya jaddada goyon bayan da aka dade ana bayarwa ga fannin kiwon lafiyar kasar.
Gudummawar ta kunshi mahimman kayayyakin kiwon lafiya na mabambantan sassan duba marasa lafiya, ciki har da na sashen warkar da cututtukan zuciya da jijiyoyin jini, da na numfashi, da sashen riga-kafin kamuwa da cututtuka, da na kula da tsarin narkewar abinci, da magungunan zazzabin cizon sauro masu yawa, da kuma magungunan yakar cututtuka.
Da yake jawabi yayin bikin mika kayayyakin, shugaban tawagar likitocin na Sin Li Zheng, ya bayyana jin dadinsa bisa bayar da gudummawar magunguna da kayayyakin aikin, da nufin inganta ayyukan asibitin, da kuma amfanar da al’ummomin yankin.
A nasa bangaren, babban jami’in kula da asibitin Augustine Tarawally, ya yaba wa tawagar ta kasar Sin bisa yadda take bayar da gudummawa ba tare da gajiyawa ba ga tsarin kiwon lafiyar Saliyo. (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post