A jiya Talata, rukunin farko na tawagar masana a fannin dakile yaduwar cututtuka ta kasar Sin ta isa birnin Kinshasa, fardar mulkin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo.
Bayan isarta kasar, tawagar masanan za ta fara bayar da taimakon jinya na tsawon watannni 3, domin tallafawa kandagarki da dakile yaduwar cutar Ebola.Wakilin ma’aikatar kiwon lafiya ta Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Luku Maleyo Marius, ya yi maraba da zuwan tawagar masanan, a filin jiragen saman kasar, inda ya ce, tawagar ta kasar Sin, ta isa Congo a daidai lokacin da ake cikin muhimmin matakin dakile yaduwar cutar Ebola, lamarin da ya nuna babban goyon baya ga gwamnati, da al’ummomin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo.
Ya ce yana fatan tawagar masanan za ta kara karfin kasar na kandagarki da dakile yaduwar cutar Ebola, tare da kara kwarewarta ta fuskar ba da jinya, domin kawo karshen annobar cikin sauri.A ranar 17 ga watan Mayun bana, hukumar kiwon lafiyar duniya WHO, ta sanar da cewa, bullar cutar Ebola a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo, babbar barazana ce ga kiwon lafiyar kasa da kasa.
Domin karfafa hadin gwiwar kasashen duniya a fannin yaki da annobar, gwamnatin kasar Sin ta tsai da kudurin aikewa da tawagar masana masu kwarewa zuwa Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo don tallafawa yaki da annobar. (Mai Fassara: Maryam Yang)














Discussion about this post