Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya dakatar da Mai Anguwar Rikadawa da ke karamar hukumar Madobi, Malam Rabi’u Yusuf, bisa zargin hannu a badakalar sayar da fili.
An sanar da dakatarwar ne ranar Laraba yayin wata zaman sauraro da Majalisar Masarautar Kano ta gudanar bayan koke-koken da aka gabatar gaban masarautar.
An isar da matakin ta bakin Waziri na Kano, Alhaji Sa’ad Shehu Gidado, bayan tattaunawa kan korafe-korafen da ke zargin an sayar da gonakin marigayi hakimin Madobi, Alhaji Sale Musa Kwankwaso, ba tare da izini ba.
A cewar korafe-korafen, an zargi Mai Anguwar da aka dakatar tare da wani dan marigayin hakimin Madobi, Isah Dahiru, da sayar da wasu sassan gonar ba tare da sani ko amincewar marigayin ba.
Da yake jawabi yayin zaman sauraron, wakilan Majalisar Masarautar Kano sun ce binciken farko ya nuna cewa Mai Anguwwar yana da hannu a cinikin filin da ake takaddama a kai. Sun bayyana lamarin a matsayin cin amana da kuma amfani da ikon sarauta ba ta yadda ya kamata ba.














Discussion about this post