Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana Shugaban Ƙasa mai ci, Bola Ahmed Tinubu, a matsayin “shugaba mara adalci”, yana mai cewa gwamnatin sa ba ta kai matsayin da ake tsammani ba a fannin tattalin arziki da shugabanci.
Atiku, wanda shi ne ɗaya daga cikin manyan jiga-jigan jam’iyyar ADC, ya yi wannan furuci ne a yammacin ranar Laraba yayin wata hira a shirin ‘Prime Time Special na ARISE News Channel’, inda ya kuma yi magana kan haɗakar jam’iyyun adawa da kuma yiwuwar kayar da Shugaba Tinubu a zaɓen 2027.
Da yake amsa tambaya kan ko manufar haɗakar ita ce kawai kawar da Tinubu daga mulki, Atiku ya ce haɗakar ta samo asali ne daga dabarun siyasa da kuma rashin gamsuwa da yadda gwamnatin ke tafiyar da al’amura.
“Bari in ce duka biyun ne, domin Bola ya kasance shugaba mara adalci, in faɗa maka gaskiya,” in ji Atiku. “Ban yi tsammanin hakan daga gare shi ba ta yadda yake tafiyar da ƙasa, ko ta fuskar tattalin arziki ko wata fuska. Abin takaici ne.”















Discussion about this post