Majalisar Dattawa ta umurci Babban Hafsan Tsaro, Olufemi Oluyede, da sauran shugabannin hukumomin tsaro da su gudanar da cikakken bincike kan ayyuka da kayan aikin sojoji bayan hare-haren da aka kai kan sansanonin soji a Benisheikh da Monguno a Jihar Borno.
Umarnin ya biyo bayan wani muhimmin kudurin gaggawa da Mataimakin shugaban mai tsawatarwa na Majalisar, Tahir Monguno (Borno ta Arewa), ya gabatar dangane da sabbin hare-haren ‘yan ta’adda a yankin Arewa maso Gabas.
Da yake gabatar da kudirin yayin zaman majalisar ranar Laraba, ɗan majalisar ya nuna matuƙar damuwa kan hare-haren baya-bayan nan da suka yi sanadin mutuwar jami’an soja da dama, ciki har da Birgediya Janar Oseni Braimoh, Kanal Mohammed Isya, Kyaftin A.M. Esmat, Laftanar Kelvin Festus, da wasu sojoji 13.
Matsayar da majalisar ta cimmawa, ta bukaci gudanar da cikakken bincike kan yadda hare-haren suka faru, ciki har da duba ko kayan aikin sojoji sun wadatar da kuma bin ƙa’idodin aikin soja yadda ya kamata.
Yayin jagorantar muhawarar, Sanata Monguno ya nuna damuwa kan yawaitar hare-hare a Monguno, wadda muhimmiyar cibiyar soji ce, da kuma Benisheikh da ke kan hanyar Damaturu zuwa Maiduguri.
Ya ce yadda hare-haren ke faruwa na nuna cewa ‘yan ta’addan na ƙoƙarin raunana ayyukan sojoji tare da kawo cikas ga ayyukan jin ƙai da harkokin kasuwanci a yankin.
A nasa jawabin, Sanatan Borno ta Kudu, Mohammed Ali Ndume, ya ce halin da ake ciki a Arewa maso Gabas yana nuna irin matsalolin tsaro da ƙasar baki ɗaya ke fuskanta, yana mai gargadin cewa ƙungiyoyin ‘yan ta’adda na ci gaba da sake fardaɗowa duk da ayyukan tsaro da ake gudanarwa a kansu.













Discussion about this post