ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsofaffin Manyan Sakatarori Sun Karrama Gwamna Lawal, Sun Yaba Da Ayyukan Ci Gaban Zamfara

by Sulaiman
6 months ago
Zamfara

Ƙungiyar Tsofaffin Manyan Sakatarori na Jihar Zamfara ta karrama Gwamna Dauda Lawal tare da yaba wa ayyukan ci gaban da gwamnatinsa ke aiwatarwa a faɗin jihar.

 

An miƙa masa lambar yabo ta girmamawa ne a ranar Juma’a a ɗakin taro na Gidan Gwamnati da ke Gusau, yayin wani taro da ya haɗa manyan tsofaffin jami’an gwamnati da suka yi wa jihar hidima tsawon shekaru.

ADVERTISEMENT
  • Ƙungiyar ‘Dikko Na Kowa Ne’ Ta Jinjina Wa Gwamnan Katsina Bisa Biyan Ƴan Fansho Haƙƙoƙinsu 
  • Burina Shi Ne Fito Da Daraja Da Mutuncin Matanmu Na Arewacin Nijeriya —Hajara Kabir

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa ƙungiyar ta bayyana manyan ayyukan ci gaba da gwamnatin Lawal ta aiwatar a matsayin dalilin ba shi wannan karramawa.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Sun nuna cewa sauye-sauyen da aka samu a fannoni da dama sun sa suka ga ya dace su girmama gwamnan bisa ƙoƙarinsa.

 

Da yake jawabi bayan karbar lambar yabon, Gwamna Lawal ya gode wa ƙungiyar bisa ganin ya cancanci wannan girmamawa, yana mai cewa babu wata karramawa da ta wuce wadda ta fito daga hannun manyan mutane da suka shafe rayuwarsu suna hidimta wa jiha cikin gaskiya da ƙwarewa.

 

Ya ce, duk da an shirya masa liyafar girmamawa, rashin lokaci ya hana hakan tabbata, amma hakan ba zai rage darajar wannan karramawa a gare shi ba. Gwamnan ya jaddada cewa gwamnatinsa na aiki ne bisa gaskiya da riƙon amana, kuma tun kafin hawansa mulki ya tsara manufofi shida da suka zamo tubalin jagorancin gwamnatinsa.

 

A cewarsa, tsaro shi ne ginshiƙin farko a cikin manufofin, kuma ana samun gagarumin ci gaba a bangaren. Ya kuma bayyana cewa ana aiwatar da ayyuka a dukkan ƙananan hukumomin jihar domin buɗe ƙofar zuba jari da habaka tattalin arziki.

 

Ya ƙara da cewa, ana sa ran kammala aikin filin jirgin saman ƙasa da ƙasa na jihar cikin ‘yan watanni masu zuwa.

 

Gwamnan ya bayyana cewa babu ƙaramar hukuma a Zamfara da ba a zuba sama da naira biliyan ashirin a ayyukan ci gaba ba, yana mai kira ga jama’a su duba ayyukan da ke gudana domin ganin sauyin da ake samu da idanunsu.

 

Haka kuma ya ce ana samun sauƙin matsalolin tsaro a hankali, yayin da kuɗaɗen shiga na cikin gida suka tashi daga kimanin Naira miliyan tamanin zuwa sama da Naira biliyan biyar.

 

Tun da farko, shugaban ƙungiyar, Muhammad Bello Umar, ya ce sun yanke shawarar karrama gwamnan ne saboda irin nasarorin da gwamnatinsa ta samu tun bayan fara aikinta a 2023.

 

Ya ce tun daga farko gwamnan ya nuna ƙwarin gwiwa da jajircewa ta hanyar fito da ajanda shida, wadda a cewarsa ta zarce tsammanin da dama.

 

Ya kuma tuna cewa a wani taronsu na baya, sun roƙi a biya bashin hakƙoƙin ritaya, kuma gwamnati ta amsa buƙatar tare da biyan sama da Naira biliyan goma sha uku da ake bin gwamnati.

 

A cewarsa, tarihin Zamfara ba zai manta da Gwamna Lawal ba saboda irin tasirin ayyukansa ga ma’aikata, lafiya, ilimi da sauran manyan ayyukan more rayuwa.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Mataimakin Shugaban Ƙasa Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar Guinea Da Switzerland

Mataimakin Shugaban Ƙasa Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar Guinea Da Switzerland

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.