ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsofaffin Manyan Sakatarori Sun Karrama Gwamna Lawal, Sun Yaba Da Ayyukan Ci Gaban Zamfara

by Sulaiman
5 months ago
Zamfara

Ƙungiyar Tsofaffin Manyan Sakatarori na Jihar Zamfara ta karrama Gwamna Dauda Lawal tare da yaba wa ayyukan ci gaban da gwamnatinsa ke aiwatarwa a faɗin jihar.

 

An miƙa masa lambar yabo ta girmamawa ne a ranar Juma’a a ɗakin taro na Gidan Gwamnati da ke Gusau, yayin wani taro da ya haɗa manyan tsofaffin jami’an gwamnati da suka yi wa jihar hidima tsawon shekaru.

ADVERTISEMENT
  • Ƙungiyar ‘Dikko Na Kowa Ne’ Ta Jinjina Wa Gwamnan Katsina Bisa Biyan Ƴan Fansho Haƙƙoƙinsu 
  • Burina Shi Ne Fito Da Daraja Da Mutuncin Matanmu Na Arewacin Nijeriya —Hajara Kabir

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa ƙungiyar ta bayyana manyan ayyukan ci gaba da gwamnatin Lawal ta aiwatar a matsayin dalilin ba shi wannan karramawa.

 

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Sun nuna cewa sauye-sauyen da aka samu a fannoni da dama sun sa suka ga ya dace su girmama gwamnan bisa ƙoƙarinsa.

 

Da yake jawabi bayan karbar lambar yabon, Gwamna Lawal ya gode wa ƙungiyar bisa ganin ya cancanci wannan girmamawa, yana mai cewa babu wata karramawa da ta wuce wadda ta fito daga hannun manyan mutane da suka shafe rayuwarsu suna hidimta wa jiha cikin gaskiya da ƙwarewa.

 

Ya ce, duk da an shirya masa liyafar girmamawa, rashin lokaci ya hana hakan tabbata, amma hakan ba zai rage darajar wannan karramawa a gare shi ba. Gwamnan ya jaddada cewa gwamnatinsa na aiki ne bisa gaskiya da riƙon amana, kuma tun kafin hawansa mulki ya tsara manufofi shida da suka zamo tubalin jagorancin gwamnatinsa.

 

A cewarsa, tsaro shi ne ginshiƙin farko a cikin manufofin, kuma ana samun gagarumin ci gaba a bangaren. Ya kuma bayyana cewa ana aiwatar da ayyuka a dukkan ƙananan hukumomin jihar domin buɗe ƙofar zuba jari da habaka tattalin arziki.

 

Ya ƙara da cewa, ana sa ran kammala aikin filin jirgin saman ƙasa da ƙasa na jihar cikin ‘yan watanni masu zuwa.

 

Gwamnan ya bayyana cewa babu ƙaramar hukuma a Zamfara da ba a zuba sama da naira biliyan ashirin a ayyukan ci gaba ba, yana mai kira ga jama’a su duba ayyukan da ke gudana domin ganin sauyin da ake samu da idanunsu.

 

Haka kuma ya ce ana samun sauƙin matsalolin tsaro a hankali, yayin da kuɗaɗen shiga na cikin gida suka tashi daga kimanin Naira miliyan tamanin zuwa sama da Naira biliyan biyar.

 

Tun da farko, shugaban ƙungiyar, Muhammad Bello Umar, ya ce sun yanke shawarar karrama gwamnan ne saboda irin nasarorin da gwamnatinsa ta samu tun bayan fara aikinta a 2023.

 

Ya ce tun daga farko gwamnan ya nuna ƙwarin gwiwa da jajircewa ta hanyar fito da ajanda shida, wadda a cewarsa ta zarce tsammanin da dama.

 

Ya kuma tuna cewa a wani taronsu na baya, sun roƙi a biya bashin hakƙoƙin ritaya, kuma gwamnati ta amsa buƙatar tare da biyan sama da Naira biliyan goma sha uku da ake bin gwamnati.

 

A cewarsa, tarihin Zamfara ba zai manta da Gwamna Lawal ba saboda irin tasirin ayyukansa ga ma’aikata, lafiya, ilimi da sauran manyan ayyukan more rayuwa.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Mataimakin Shugaban Ƙasa Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar Guinea Da Switzerland

Mataimakin Shugaban Ƙasa Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar Guinea Da Switzerland

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.