ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mataimakin Shugaban Ƙasa Shettima Ya Dawo Abuja Bayan Ziyarar Guinea Da Switzerland

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Shettima

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya dawo birnin Abuja bayan kammala wata ziyarar diflomasiyya da tattalin arziƙi ta tsawon mako guda zuwa Guinea-Conakry da kuma Switzerland, inda ya bayyana cewa Nijeriya ta dawo sahun gaba a tattaunawar manufofin tattalin arziƙi na duniya da na yankin.

A cewar wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Stanley Nkwocha, ya bayyana cewa Shettima ya sauka a Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe a ranar Asabar, bayan ya wakilci Shugaba Bola Tinubu a bikin rantsar da Shugaban Ƙasar Guinea, Mamadi Doumbouya, tare da jagorantar tawagar Nijeriya zuwa taron shekara-shekara karo na 56 na Dandalin Tattalin Arziƙin Duniya (WEF) da aka gudanar a Davos, Switzerland.

  • Me Ya Sa Masu Koyarwa ‘Yan Asalin Ingila Ba Sa Iya Lashe Kofin Premier?
  • Shettima Ya Ce Zuba Jari A Ɓangaren  Ilimi Ba Caca Ba Ce

Shettima ya ce wannan ziyara na daga cikin ƙudirin Nijeriya na ƙarfafa haɗin kai a yankin Yammacin Afirka da kuma sake fasalin tattalin arziƙin ƙasa ƙarƙashin ajandar “Renewed Hope” ta Shugaba Tinubu. Ya ƙara da cewa halartar bikin rantsar da Shugaba Doumbouya ya sake jaddada rawar jagorancin Nijeriya a ECOWAS da buɗe sabbin hanyoyin haɗin gwuiwa a fannonin noma da masana’antu.

ADVERTISEMENT

Daga Guinea, Mataimakin Shugaban Ƙasar ya tafi Davos inda ya jagoranci tawagar Nijeriya a taron WEF 2026. Daga cikin muhimman abubuwan da suka faru akwai ƙaddamar da “Nigeria House Davos,” wato katafaren baje kolin Nijeriya na farko a dandalin Davos, wanda aka tsara domin jawo masu zuba jari a fannonin ma’adinai, da noma da tattalin arziƙin zamani a fannin dijital.

A wani taro na musamman kan batun tsaron abinci, Shettima ya bayyana sabon tsarin Nijeriya kan wadatar abinci, yana mai bayyana noma a matsayin ginshiƙin tsaron ƙasa da daidaiton tattalin arziƙi. Ya kuma shaida wa masu zuba jari cewa alamomin tattalin arziƙin Nijeriya na farfaɗowa, inda ya yi hasashen bunƙasar GDP da kuma raguwar hauhawar farashi, tare da nuna cewa ƙasar na gab da zama mai fitar da man fetur da aka tace, tare da ƙara fitar da sauran kaya da ma’aikatan fasahar dijital zuwa kasuwannin duniya.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Shettima
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
  • Abubakar Sulaiman
    Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka
  • Abubakar Sulaiman
    Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
NNPP Ta Caccaki Gwamna Yusuf Kan Ficewa Daga Jam’iyyar, Ta Ce “Cin Amanar Kano Da Kwankwasiyya Ne”

NNPP Ta Caccaki Gwamna Yusuf Kan Ficewa Daga Jam’iyyar, Ta Ce “Cin Amanar Kano Da Kwankwasiyya Ne”

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.