Yau Jumma’a, an bude dandalin tattauna shugabancin kasa na cibiyoyin bincike na kasashe masu tasowa na 2026 a nan birnin Beijing.
A taron na wannan karo, ana mai da hankali kan batutuwa kamar hanyar samun zamanantarwa, da hadin kan kasashe masu tasowa, da matsayin aiki na jam’iyyun siyasa a kan tsarin mulkin kasa, da jagorantar akida a cikin gyare-gyaren tsarin mulkin duniya, da kuma horar da matasa.
Mutane sama da 100 ne daga kasashe da kungiyoyin kasa da kasa sama da 20 suka halarci taron, wadanda suka hada da manyan jami’an jam’iyyu, da kwararru, da masana da sauransu.
A ciki kuma, Erik Solheim, shugaban cibiyar Asiya ta kungiyar EU, kana tsohon mataimakin babban sakataren MDD, kuma daraktan hukumar kiyaye muhalli ta MDD wato UNEP, ya bayyana a wata hira da wakilin babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG cewa, Sin ta dade tana himmatuwa wajen samun ci gaban cikin gida, kuma bisa ci gabanta, ta ba da gudummawa ga ci gaban tattalin arzikin duniya.
Bugu da kari, nasarorin da Sin ta samu wajen magance matsalolin muhalli suna sahun gaba a duk fadin duniya. Ya ce, abun da dabarun Sin suka kawo wa duniya shi ne, jagoranci mai karfi yana da matukar muhimmanci, kuma karfin kasa shi ma wani muhimmin lamari ne.(Safiyah Ma)













