Bisa labarin da aka bayar, an ce, jagoran yankin Taiwan na kasar Sin Lai Ching-te ya isa kasar Eswatini cikin jirgin saman sarkin kasar ta Eswatini a yau Asabar.
A lokacin da kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ke amsa tambayar manema labarai a kan batun, ya yi nuni da cewa, sa’o’i kadan bayan aukuwar girgizar kasa a gundumar Yilan da ke Taiwan, sai Lai Ching-te ya kyale al’ummar da bala’in ya ritsa da su, ya sulale a boye zuwa Eswatini, inda hakan ya kara sa shi zama abin dariya a duniya.
Kakakin ya kara da cewa, abubuwan da suka faru ga Lai Ching-te da ma ‘yan tsirarrunsa a wannan ziyara sun sake shaida cewa, tuni manufar Sin daya tak a duniya ta zama tushen huldar kasa da kasa, wadda kuma ta samu amincewa daga daukacin kasashen duniya.
Jam’iyyar DPP ba za ta kai ga cimma burinta ba duk da kokarin da take yi na hada hannu da wasu kasashen waje ko kuma renonsu ta wasu hanyoyi, kuma ko ta yaya ba za ta kai ga canja gaskiyar yanayin kasancewar yankin Taiwan wani bangare na kasar Sin ba.
Kazalika, duk kokarin da ‘yan aware na Taiwan suke, ba za su gyara yanayin yadda al’ummun duniya ke kyamarsu ba.















Discussion about this post