Wani uba da ‘yarsa matashiya sun rasa rayukansu bayan sun faɗa cikin wata tsohuwar rijiya da aka daina amfani da ita a ƙauyen Yancibi, ƙaramar hukumar Tsanyawa ta Jihar Kano.
Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata, ga mahaifin budurwar, Abubakar Abdullahi mai kimanin shekaru 45 da ‘yarsa mai shekaru 15, Fiddausi.
Jami’in Hulɗa da Jama’a na Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, Saminu Yusuf Abdullahi, ya ce Fiddausi ta zame ne, inda ta faɗa cikin rijiyar.Sannan shi kuma mahaifinta, a yayin ƙoƙarin ceto ta, shi ma ya faɗa cikin rijiyar.
Abdullahi ya ce jami’an ceto daga ofishin Hukumar Kashe Gobara na Tsanyawa sun isa wurin cikin gaggawa, amma saboda duhu da kuma mawuyacin halin da wurin yake ciki, ba a yi nasarar ciro su a raye ba.
A cewarsa, an miƙa gawarwakin ga Hakimin ƙauyen Yancibi, Shamsu Sani.
Daga ƙarshe, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan, tare da yin kira ga al’umma da su guji shiga cikin rijiyoyi ba tare da ingantattun kayan aikin ceto ba.














