A ranar Juma’a 19 ga watan ne aka gudanar da taron tunawa da cika shekaru 20 da kafa majalisar kare hakkin dan Adam ta Majalisar Dinkin Duniya ko (UNHRC), a birnin Geneva na Switzerland. Inda jakadan kasar Sin a ofishin Majalisar Dinkin Duniya dake Geneva, Jia Guide, ya gabatar da jawabi, yana mai cewa shawarar inganta jagorancin harkokin duniya da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, tana da ma’ana matuka ga yunkurin kyautata ayyukan majalisar ta UNHRC.
A cewar jami’in na kasar Sin, domin daidaita ayyukan UNHRC, ya kamata a girmama ka’idojin tabbatar da daidaiton ikon mulkin kai na mabambantan kasashe, da bin dokokin kasa da kasa, da nuna adalci da sanin-ya-kamata, da shawarwari don kulla huldar hadin kai da samun ci gaban al’amura, da dai sauransu.Ban da haka, ya ce ya kamata a samar da cikakkiyar kulawa ga mutane, da aiwatar da manufar samar da mabambantan bangarori masu fada-a-ji a duniya, da samar da daidaito tsakanin hakkin dan Adam na fannonin siyasa da tattalin arziki, da na al’adu.
Jami’in Sin ya kara da cewa, kamata ya yi, a girmama ikon kasashe daban daban na zabar turbar da suke bi wajen raya hakkin dan Adam. Kana a nata bangare, gwamnatin kasar Sin ta dora matukar muhimmanci kan karewa, da inganta hakkin dan Adam. Ya ce kasar Sin na son yin hadin gwiwa tare da kasashe daban daban, wajen daidaita ayyukan kare hakkin dan Adam a duniya, da gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai daya. (Bello Wang)















Discussion about this post