A kwanakin baya, hadaddiyar kungiyar raya harkoki masu alaka da Majalisar Dinkin Duniya ta kasar Sin (UNA-CHINA), da tawagar kasar Sin a ofishin Majalisar Dinkin Duniya dake birnin Geneva na kasar Switzerland, sun shirya wani taro a gefen taro karon 62, na majalisar raya hakkin dan Adam ta Majalisar Dinkin Duniya, don tattauna batun kare hakkin dan Adam da kyautata tsarin jagorancin duniya.
Baki kimanin 50, daga tawagogin kasashe daban daban dake birnin Geneva, da ofishin kwamishina mai kula da aikin kare hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya, da kungiyoyin jama’a sun halarci taro, inda suka nuna cewa, ya kamata gamayyar kasa da kasa su kara kokarin hadin gwiwa da juna don neman karewa, da raya hakkin dan Adam.
Sun kuma ce kasar Sin tana taka rawar gani a fannin hadin gwiwa da sauran kasashe, don kyautata yanayin kare hakkin dan Adam a duniya, ta yadda za a kafa wani tsari mai cike da adalci da sanin-ya-kamata, da yunkuri na kula da hakkin al’ummun kasashe daban daban.Manyan baki mahalarta taron sun kuma kara da cewa, wata takardar bayani da kasar Sin ta gabatar a kwanakin baya, ta shaida kokarin da kasar ke yi, na aiwatar da akidar “raya hakkin dan Adam ta hanyar ci gaban tattalin arziki”. (Bello Wang)














Discussion about this post