Wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Fu Cong, ya yi kira ga bangarori masu ruwa da tsaki da su cika yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza gaba daya, tare da cimma cikakkiyar yarjejeniyar tsagaita wuta ta dindindin a Gaza.
Fu Cong ya yi kiran ne cikin jawabin da ya gabatar a jiya Alhamis 21 ga watan nan, yayin taron kwamitin sulhun MDD kan batun Falasdinu da Isra’ila.
Fu Cong ya kara da cewa, tun bayan da aka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta, kusan kullum Isra’ila na kaddamar da hare-hare, wanda hakan ya yi sanadiyar mutuwar mutane fiye da 870.
Fu ya kuma ce dole ne Isra’ila ta sauke nauyin dake wuyanta na wajibi, a matsayinta na kasar da ta yi mamaya, karkashin dokar jin kai ta kasa da kasa, ta kuma soke takunkumin shigar da kayan agaji, ta ba da izinin shigar da magunguna, da sauran kayayyakin da ake bukata cikin gaggawa, da man fetur, da kayan bukata na tsugunar da wadanda hare-hare ke ritsawa da su a Gaza da sauransu.Kazalika, Fu Cong ya ce, “tsarin kafa kasashe biyu” shi ne hanya daya tilo da za a iya bi don magance matsalar Falasdinu.
Kuma bangaren Sin yana fatan yin hadin gwiwa tare da al’ummun kasa da kasa, don kokarin cimma cikakkiyar yarjejeniyar tsagaita wuta ta dindindin a Gaza, da sassauta matsalar jin kai, da aiwatar da “tsarin kafa kasashe biyu”, da kuma cimma cikakkiyar mafita mai adalci, da gaggauta shawo kan matsalar Falasdinu. (Amina Xu)















Discussion about this post