ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Lawal Ya Zama Ɗan Takarar APC A Zamfara, Ya Yi Alƙawarin Ƙara Ayyukan Ci Gaba

by Sulaiman
1 month ago
APC

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi alƙawarin ci gaba da ƙara ayyukan raya ƙasa domin inganta rayuwar al’ummar jihar.A ranar Alhamis ne gwamnan ya zama ɗan takarar jam’iyyar APC domin zaɓen gwamnan jihar Zamfara na shekarar 2027.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa shugaban kwamitin zaɓen fidda gwani na gwamna na APC a Zamfara, Alhaji Babagana Uba, ya sanar da cewa an amince da Gwamna Dauda Lawal a matsayin ɗan takarar jam’iyyar baki ɗaya bayan samun ƙuri’u 301,893.

Sanarwar ta ƙara da cewa, an gudanar da amincewar ne a dukkan ƙananan hukumomi 14 na jihar Zamfara, tare da sa ido daga jami’an Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC).

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ce: “Kwamitin zaɓen fidda gwani na gwamnan jihar Zamfara ya ayyana Gwamna Dauda Lawal a matsayin ɗan takarar jam’iyyar APC shi kaɗai domin babban zaɓen shekarar 2027.

“Kwamitin ya karɓi sakamakon amincewa daga jami’an tattara sakamako na dukkan ƙananan hukumomi 14 na jihar, waɗanda Malam Abubakar Mohammed Nakwada, shugaban tattara sakamako na APC a jihar, tare da sauran mambobin tawagar tattara sakamako suka sanya wa hannu.”

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Shugaban kwamitin ya kuma bayyana sakamakon amincewar da aka samu daga ƙananan hukumomi daban-daban kamar haka: Anka 16,607; Bakura 18,112; Birnin Magaji 15,440; Bukkuyum 11,406; Bungudu 24,406; Gummi 23,024; Gusau 61,072; Kaura Namoda 18,315; Maradun 15,624; Maru 17,341; Shinkafi 15,204; Talata Mafara 22,884; Tsafe 19,354; da Zurmi 22,506.Da yake jawabi bayan ayyana shi a matsayin ɗan takara, Gwamna Dauda Lawal ya gode wa al’ummar Zamfara bisa amincewa da goyon bayan da suka nuna masa.

Ya ce, gwamnatinsa za ta ci gaba da aiwatar da ayyukan raya ƙasa a fannoni daban-daban da suka haɗa da ilimi, lafiya, ababen more rayuwa da tattalin arziki.

“A yau rana ce mai tarihi a siyasar jihar Zamfara, domin dukkan manyan masu ruwa da tsaki sun haɗu ƙarƙashin inuwa ɗaya cikin haɗin kai,” in ji gwamnan.

“Da aka ayyana ni a matsayin ɗan takarar jam’iyyarmu ta APC, ina godiya ga dukkan mambobin jam’iyya da al’ummar jihar bisa amincewar da suka yi da gwamnatina.

“Wannan gagarumin goyon baya da soyayya da aka nuna mini zai ƙara ƙarfafa mini gwiwa wajen ci gaba da ƙoƙarin ceto da sake gina jihar Zamfara.

“Ina kuma godiya ga shugaban kwamitin zaɓen fidda gwani da sauran mambobinsa da suka tabbatar da gudanar da zaɓen cikin nasara a jihar Zamfara.”

APC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Kashe Ƴansanda Da Sojoji 17 A Yobe

Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Kashe Ƴansanda Da Sojoji 17 A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.