ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Lawal Ya Zama Ɗan Takarar APC A Zamfara, Ya Yi Alƙawarin Ƙara Ayyukan Ci Gaba

by Sulaiman
2 months ago
APC

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi alƙawarin ci gaba da ƙara ayyukan raya ƙasa domin inganta rayuwar al’ummar jihar.A ranar Alhamis ne gwamnan ya zama ɗan takarar jam’iyyar APC domin zaɓen gwamnan jihar Zamfara na shekarar 2027.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa shugaban kwamitin zaɓen fidda gwani na gwamna na APC a Zamfara, Alhaji Babagana Uba, ya sanar da cewa an amince da Gwamna Dauda Lawal a matsayin ɗan takarar jam’iyyar baki ɗaya bayan samun ƙuri’u 301,893.

Sanarwar ta ƙara da cewa, an gudanar da amincewar ne a dukkan ƙananan hukumomi 14 na jihar Zamfara, tare da sa ido daga jami’an Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC).

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ce: “Kwamitin zaɓen fidda gwani na gwamnan jihar Zamfara ya ayyana Gwamna Dauda Lawal a matsayin ɗan takarar jam’iyyar APC shi kaɗai domin babban zaɓen shekarar 2027.

“Kwamitin ya karɓi sakamakon amincewa daga jami’an tattara sakamako na dukkan ƙananan hukumomi 14 na jihar, waɗanda Malam Abubakar Mohammed Nakwada, shugaban tattara sakamako na APC a jihar, tare da sauran mambobin tawagar tattara sakamako suka sanya wa hannu.”

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

Shugaban kwamitin ya kuma bayyana sakamakon amincewar da aka samu daga ƙananan hukumomi daban-daban kamar haka: Anka 16,607; Bakura 18,112; Birnin Magaji 15,440; Bukkuyum 11,406; Bungudu 24,406; Gummi 23,024; Gusau 61,072; Kaura Namoda 18,315; Maradun 15,624; Maru 17,341; Shinkafi 15,204; Talata Mafara 22,884; Tsafe 19,354; da Zurmi 22,506.Da yake jawabi bayan ayyana shi a matsayin ɗan takara, Gwamna Dauda Lawal ya gode wa al’ummar Zamfara bisa amincewa da goyon bayan da suka nuna masa.

Ya ce, gwamnatinsa za ta ci gaba da aiwatar da ayyukan raya ƙasa a fannoni daban-daban da suka haɗa da ilimi, lafiya, ababen more rayuwa da tattalin arziki.

“A yau rana ce mai tarihi a siyasar jihar Zamfara, domin dukkan manyan masu ruwa da tsaki sun haɗu ƙarƙashin inuwa ɗaya cikin haɗin kai,” in ji gwamnan.

“Da aka ayyana ni a matsayin ɗan takarar jam’iyyarmu ta APC, ina godiya ga dukkan mambobin jam’iyya da al’ummar jihar bisa amincewar da suka yi da gwamnatina.

“Wannan gagarumin goyon baya da soyayya da aka nuna mini zai ƙara ƙarfafa mini gwiwa wajen ci gaba da ƙoƙarin ceto da sake gina jihar Zamfara.

“Ina kuma godiya ga shugaban kwamitin zaɓen fidda gwani da sauran mambobinsa da suka tabbatar da gudanar da zaɓen cikin nasara a jihar Zamfara.”

APC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa
Siyasa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Next Post
Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Kashe Ƴansanda Da Sojoji 17 A Yobe

Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Kashe Ƴansanda Da Sojoji 17 A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.