ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Lawal Ya Zama Ɗan Takarar APC A Zamfara, Ya Yi Alƙawarin Ƙara Ayyukan Ci Gaba

by Sulaiman
2 weeks ago
APC

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi alƙawarin ci gaba da ƙara ayyukan raya ƙasa domin inganta rayuwar al’ummar jihar.A ranar Alhamis ne gwamnan ya zama ɗan takarar jam’iyyar APC domin zaɓen gwamnan jihar Zamfara na shekarar 2027.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa shugaban kwamitin zaɓen fidda gwani na gwamna na APC a Zamfara, Alhaji Babagana Uba, ya sanar da cewa an amince da Gwamna Dauda Lawal a matsayin ɗan takarar jam’iyyar baki ɗaya bayan samun ƙuri’u 301,893.

Sanarwar ta ƙara da cewa, an gudanar da amincewar ne a dukkan ƙananan hukumomi 14 na jihar Zamfara, tare da sa ido daga jami’an Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC).

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ce: “Kwamitin zaɓen fidda gwani na gwamnan jihar Zamfara ya ayyana Gwamna Dauda Lawal a matsayin ɗan takarar jam’iyyar APC shi kaɗai domin babban zaɓen shekarar 2027.

“Kwamitin ya karɓi sakamakon amincewa daga jami’an tattara sakamako na dukkan ƙananan hukumomi 14 na jihar, waɗanda Malam Abubakar Mohammed Nakwada, shugaban tattara sakamako na APC a jihar, tare da sauran mambobin tawagar tattara sakamako suka sanya wa hannu.”

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Shugaban kwamitin ya kuma bayyana sakamakon amincewar da aka samu daga ƙananan hukumomi daban-daban kamar haka: Anka 16,607; Bakura 18,112; Birnin Magaji 15,440; Bukkuyum 11,406; Bungudu 24,406; Gummi 23,024; Gusau 61,072; Kaura Namoda 18,315; Maradun 15,624; Maru 17,341; Shinkafi 15,204; Talata Mafara 22,884; Tsafe 19,354; da Zurmi 22,506.Da yake jawabi bayan ayyana shi a matsayin ɗan takara, Gwamna Dauda Lawal ya gode wa al’ummar Zamfara bisa amincewa da goyon bayan da suka nuna masa.

Ya ce, gwamnatinsa za ta ci gaba da aiwatar da ayyukan raya ƙasa a fannoni daban-daban da suka haɗa da ilimi, lafiya, ababen more rayuwa da tattalin arziki.

“A yau rana ce mai tarihi a siyasar jihar Zamfara, domin dukkan manyan masu ruwa da tsaki sun haɗu ƙarƙashin inuwa ɗaya cikin haɗin kai,” in ji gwamnan.

“Da aka ayyana ni a matsayin ɗan takarar jam’iyyarmu ta APC, ina godiya ga dukkan mambobin jam’iyya da al’ummar jihar bisa amincewar da suka yi da gwamnatina.

“Wannan gagarumin goyon baya da soyayya da aka nuna mini zai ƙara ƙarfafa mini gwiwa wajen ci gaba da ƙoƙarin ceto da sake gina jihar Zamfara.

“Ina kuma godiya ga shugaban kwamitin zaɓen fidda gwani da sauran mambobinsa da suka tabbatar da gudanar da zaɓen cikin nasara a jihar Zamfara.”

APC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Kashe Ƴansanda Da Sojoji 17 A Yobe

Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Kashe Ƴansanda Da Sojoji 17 A Yobe

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.