Babban jami’in diflomasiyar kasar Sin, Wang Yi, ya bayyana cewa, yayin da ake fuskantar gagaruman sauye-sauye da yanayi mai sarkakiya a fagen kasa da kasa, Sin a shirye take ta hada hannu da sauran mambobin BRICS domin tinkarar kalubalen da ke fuskantar bil’adama tare da tsayawa tsayin daka kan tafarkin ci gaban duniya mai dimbin tarihi.
Wang, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake halartar taron masu ba da shawara kan harkokin tsaro na kasashen BRICS da manyan wakilai kan harkokin tsaron kasa karo na 16, a kasar Indiya.
Wang ya kuma bukaci kasashen BRICS da su dauki matakin magance kalubalen da duniya ke fuskanta, da suka hada da tsayawa kaifi daya wajen yaki da duk wani nau’in ta’addanci, da dakile matsalolin makamashi da wadatar abinci a duniya yadda ya kamata, da kuma yin hadin gwiwa wajen tinkarar barkewar cutar Ebola a Afirka. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post