Memba a ofishin siyasa na kwamitin tsakiyar jam’iyyar kwaminis ta Sin JKS, kuma ministan harkokin wajen kasar Mr. Wang Yi, ya gana da ministan harkokin wajen kasar Seychelles Barry Faure a jiya Litinin a nan birnin Beijing.
Yayin tattaunawarsu, Wang Yi ya bayyana cewa, kwanan nan gwamnatin Seychelles tare da tarin gwamnatocin kasashe kawayenta, sun soke izinin saukar jirgin saman wakilin ‘yan awaren na Taiwan Lai Ching-te a kasashensu, bisa doka da ka’ida a fili.
Har ila yau, bangaren Seychelles ya fitar da sanarwa, inda ya bayyana tsattsauran matsayinsa a fili dangane da rungumar manufar “kasancewar kasar Sin daya tak a duniya”. Kuma bangaren Sin yana matukar yabawa da wannan mataki. Wang Yi ya kuma yi imanin cewa, kasashe da yawa za su yi koyi da Seychelles, tare da tsayawa a bangaren adalci da daidaitaccen tarihi.
Wang Yi ya kara da cewa, bangaren Sin yana son yin amfani da damar cika shekaru 50 da kulla alakar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu, don ciyar da hadin gwiwa a fannoni kamar na raya tattalin arzikin dijital, da tattalin arzikin teku, da tattalin arzikin tsibirai, da tattalin arziki na bola jari, da kuma ciyar da cikakkiyar dangantakar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Seychelles zuwa sabon matsayi.
Ya ce bangaren Sin zai ci gaba da goyon bayan Seychelles, wajen kare ikonsa na mallakar kasa, da ‘yancin kai, da hakkokin da suka dace, da kuma goyon bayan Seychelles wajen taka babbar rawa a harkokin shiyyarta da ma na duniya baki daya.
A nasa bangaren, Barry Faure ya bayyana cewa, cikin shekaru 50 da kulla alakar diflomasiyya tsakaninsu, har kullum kasar Sin ta kasance tana cudanya tare da Seychelles bisa adalci da daidaito, kuma ta ba da muhimmin taimako ga ci gaban tattalin arziki da zamantakewa na Seychelles.
Har ila yau, bangaren Seychelles yana godiya ga hakan. Kazalika, ya sake jaddada tsayawa tsayin daka kan manufar “kasancewar kasar Sin daya tak a duniya”.
Bangaren Seychelles yana goyon bayan manyan shawarwari guda hudu na raya duniya da shugaba Xi Jinping ya gabatar, kuma yana godiya ga bangaren Sin bisa matakin soke gaba dayan haraji kan hajojin dukkan kasashen Afirka 53 da ke da huldar diplomasiyya da Sin, kuma yana fatan yin amfani da wannan manufa mai fa’idar sosai, don amfanin al’ummominsu. (Amina Xu)















Discussion about this post