Shugaban jam’iyyar ADC), David Mark, ya bayyana cewa ficewar manyan ‘yan siyasa kamar Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso zai sa jam’iyyar ta ƙara himma domin samun nasara a zaɓen 2027.
Mark ya yi wannan bayani ne yayin da yake jawabi ga mambobin tsofaffin ‘yan majalisar dokokin tarayya na jam’iyyar ADC a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja.
Ya jaddada cewa duk da tasirin da ficewar jagororin biyu zai yi, hakan zai zama wani ƙarfafawa ga jam’iyyar domin ta sake tsara kanta da ƙarfafa shirinta na zaɓe.
“Babu shakka, ficewar Obi da Kwankwaso yana da tasiri, amma hakan zai ƙara sa mu dage mu yi aiki tuƙuru,” in ji Mark.
Ya kuma tabbatar da cewa jam’iyyar za ta shawo kan ƙalubalen da take fuskanta a yanzu, tare da bayyana cewa hakan zai taimaka wajen ƙarfafa ta domin samun nasara a zaɓukan da ke tafe.















Discussion about this post