A jiya Litinin ne memba a ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya yi bayani game da ziyarar aiki da ya gudanar a kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU, da kasashen Habasha, Tanzaniya, da kuma Lesotho.
A yayin ziyararsa, Wang Yi ya yi shawarwari kan manyan tsare-tsare tsakanin Sin da AU a hedkwatar kungiyar AU, inda aka kaddamar da shekarar musayar al’adu da cudanyar jama’a a tsakanin Sin da Afirka ta shekarar 2026. Dangane da wannan harka, Wang Yi ya ce, kaddamar da shekarar musayar al’adu da cudanyar jama’a a tsakanin Sin da Afirka, muhimman matakai ne da aka dauka, tun bayan tattaunawa tsakanin shugaba Xi Jinping da shugabannin kasashen Afirka. Ya ce, “Za mu gudanar da aikace-aikace na mu’amala kimanin 600, domin kara fahimtar jama’ar kasashen Afirka kan kyakkyawan zumuncin dake tsakanin kasar Sin da kasashen nahiyar”.
Haka kuma, ya ce, nasarori da ci gaban da kasashen Afirka suka samu, ya sa shi farin ciki kwarai da gaske, kana, manyan kasuwanni a kasar Sin za su samar da damammaki masu kyau ga kasashen Afirka. A yayin taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka da aka yi a birnin Beijing a shekarar 2024, shugaba Xi Jinping ya gabatar da shirin neman zamanantarwa a manyan fannoni guda 6 bisa hadin gwiwar Sin da Afirka, wanda ya ba da jagoranci ga yadda za a raya dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka. Kana, abubuwan da ya ji, da kuma wadanda ya gani a kasashen Afirka, sun ba shi tabbacin cewa kasashen Sin da Afirka za su cimma makoma mai haske a fannin neman zamanantarwa.
Da yake tsokaci game da yadda aka aiwatar da sakamakon taron kolin dandalin FOCAC na Beijing, Wang Yi ya ce, a halin yanzu, an riga an kaddamar da shirye-shirye har kaso 90 bisa dari na sakamakon da aka cimma a yayin taron.
Ban da haka kuma, Wang Yi ya ce, kasar Sin za ta ci gaba da kasance muhimmiyar kasa da ta inganta bunkasar tattalin arzikin duniya. Tana kuma fatan ba da taimako ga kasashen Afirka wajen neman ci gaba da farfadowa. Shugabannin kasashen Afirka sun jinjinawa kasar Sin game da nasarorin da ta cimma, suna kuma sa ran zamanantar da kasar Sin zai tallafa wa kasashen Afirka.
A yayin ziyararsa a wannan karo, kungiyar AU da kasashen da abin ya shafa, dukkansu sun fitar da sanawar hadin gwiwa da kasar Sin, inda suka nuna goyon baya ga Sin kan kare manufar “kasancewar kasar Sin daya tak a duniya”. Wang Yi ya ce, lamarin da ya sake nuna cewa, shimfida dunkulewar kasar Sin baki daya ya dace da ra’ayin al’ummomin duniya, da halin da muke ciki. Kasar Sin za ta mayar da martani ga duk wani bangare daga kasashen waje, dake son tsoma baki kan batun Taiwan, da kuma tsoma baki kan harkokin cikin gidan kasar Sin, kuma irin wadannan sassa ba za su cimma nasara ba. (Mai Fassara: Maryam Yang)















Discussion about this post