ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Ya Yi Bayani Game Da Ziyarar Aikinsa A Wasu Kasashen Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Wang yi

A jiya Litinin ne memba a ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya yi bayani game da ziyarar aiki da ya gudanar a kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU, da kasashen Habasha, Tanzaniya, da kuma Lesotho.

A yayin ziyararsa, Wang Yi ya yi shawarwari kan manyan tsare-tsare tsakanin Sin da AU a hedkwatar kungiyar AU, inda aka kaddamar da shekarar musayar al’adu da cudanyar jama’a a tsakanin Sin da Afirka ta shekarar 2026. Dangane da wannan harka, Wang Yi ya ce, kaddamar da shekarar musayar al’adu da cudanyar jama’a a tsakanin Sin da Afirka, muhimman matakai ne da aka dauka, tun bayan tattaunawa tsakanin shugaba Xi Jinping da shugabannin kasashen Afirka. Ya ce, “Za mu gudanar da aikace-aikace na mu’amala kimanin 600, domin kara fahimtar jama’ar kasashen Afirka kan kyakkyawan zumuncin dake tsakanin kasar Sin da kasashen nahiyar”.

Haka kuma, ya ce, nasarori da ci gaban da kasashen Afirka suka samu, ya sa shi farin ciki kwarai da gaske, kana, manyan kasuwanni a kasar Sin za su samar da damammaki masu kyau ga kasashen Afirka. A yayin taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka da aka yi a birnin Beijing a shekarar 2024, shugaba Xi Jinping ya gabatar da shirin neman zamanantarwa a manyan fannoni guda 6 bisa hadin gwiwar Sin da Afirka, wanda ya ba da jagoranci ga yadda za a raya dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka. Kana, abubuwan da ya ji, da kuma wadanda ya gani a kasashen Afirka, sun ba shi tabbacin cewa kasashen Sin da Afirka za su cimma makoma mai haske a fannin neman zamanantarwa.

ADVERTISEMENT

Da yake tsokaci game da yadda aka aiwatar da sakamakon taron kolin dandalin FOCAC na Beijing, Wang Yi ya ce, a halin yanzu, an riga an kaddamar da shirye-shirye har kaso 90 bisa dari na sakamakon da aka cimma a yayin taron.

Ban da haka kuma, Wang Yi ya ce, kasar Sin za ta ci gaba da kasance muhimmiyar kasa da ta inganta bunkasar tattalin arzikin duniya. Tana kuma fatan ba da taimako ga kasashen Afirka wajen neman ci gaba da farfadowa. Shugabannin kasashen Afirka sun jinjinawa kasar Sin game da nasarorin da ta cimma, suna kuma sa ran zamanantar da kasar Sin zai tallafa wa kasashen Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

A yayin ziyararsa a wannan karo, kungiyar AU da kasashen da abin ya shafa, dukkansu sun fitar da sanawar hadin gwiwa da kasar Sin, inda suka nuna goyon baya ga Sin kan kare manufar “kasancewar kasar Sin daya tak a duniya”. Wang Yi ya ce, lamarin da ya sake nuna cewa, shimfida dunkulewar kasar Sin baki daya ya dace da ra’ayin al’ummomin duniya, da halin da muke ciki. Kasar Sin za ta mayar da martani ga duk wani bangare daga kasashen waje, dake son tsoma baki kan batun Taiwan, da kuma tsoma baki kan harkokin cikin gidan kasar Sin, kuma irin wadannan sassa ba za su cimma nasara ba. (Mai Fassara: Maryam Yang)

 

Wang yi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Wang yi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Gwamnatin Ƙasar Gabon Ta Ɗage Dakatarwar Da Ta Yi Wa Aubameyang

Gwamnatin Ƙasar Gabon Ta Ɗage Dakatarwar Da Ta Yi Wa Aubameyang

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.