ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi Ya Yi Bayani Game Da Ziyarar Aikinsa A Wasu Kasashen Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
Wang yi

A jiya Litinin ne memba a ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya yi bayani game da ziyarar aiki da ya gudanar a kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU, da kasashen Habasha, Tanzaniya, da kuma Lesotho.

A yayin ziyararsa, Wang Yi ya yi shawarwari kan manyan tsare-tsare tsakanin Sin da AU a hedkwatar kungiyar AU, inda aka kaddamar da shekarar musayar al’adu da cudanyar jama’a a tsakanin Sin da Afirka ta shekarar 2026. Dangane da wannan harka, Wang Yi ya ce, kaddamar da shekarar musayar al’adu da cudanyar jama’a a tsakanin Sin da Afirka, muhimman matakai ne da aka dauka, tun bayan tattaunawa tsakanin shugaba Xi Jinping da shugabannin kasashen Afirka. Ya ce, “Za mu gudanar da aikace-aikace na mu’amala kimanin 600, domin kara fahimtar jama’ar kasashen Afirka kan kyakkyawan zumuncin dake tsakanin kasar Sin da kasashen nahiyar”.

Haka kuma, ya ce, nasarori da ci gaban da kasashen Afirka suka samu, ya sa shi farin ciki kwarai da gaske, kana, manyan kasuwanni a kasar Sin za su samar da damammaki masu kyau ga kasashen Afirka. A yayin taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka da aka yi a birnin Beijing a shekarar 2024, shugaba Xi Jinping ya gabatar da shirin neman zamanantarwa a manyan fannoni guda 6 bisa hadin gwiwar Sin da Afirka, wanda ya ba da jagoranci ga yadda za a raya dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka. Kana, abubuwan da ya ji, da kuma wadanda ya gani a kasashen Afirka, sun ba shi tabbacin cewa kasashen Sin da Afirka za su cimma makoma mai haske a fannin neman zamanantarwa.

ADVERTISEMENT

Da yake tsokaci game da yadda aka aiwatar da sakamakon taron kolin dandalin FOCAC na Beijing, Wang Yi ya ce, a halin yanzu, an riga an kaddamar da shirye-shirye har kaso 90 bisa dari na sakamakon da aka cimma a yayin taron.

Ban da haka kuma, Wang Yi ya ce, kasar Sin za ta ci gaba da kasance muhimmiyar kasa da ta inganta bunkasar tattalin arzikin duniya. Tana kuma fatan ba da taimako ga kasashen Afirka wajen neman ci gaba da farfadowa. Shugabannin kasashen Afirka sun jinjinawa kasar Sin game da nasarorin da ta cimma, suna kuma sa ran zamanantar da kasar Sin zai tallafa wa kasashen Afirka.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

A yayin ziyararsa a wannan karo, kungiyar AU da kasashen da abin ya shafa, dukkansu sun fitar da sanawar hadin gwiwa da kasar Sin, inda suka nuna goyon baya ga Sin kan kare manufar “kasancewar kasar Sin daya tak a duniya”. Wang Yi ya ce, lamarin da ya sake nuna cewa, shimfida dunkulewar kasar Sin baki daya ya dace da ra’ayin al’ummomin duniya, da halin da muke ciki. Kasar Sin za ta mayar da martani ga duk wani bangare daga kasashen waje, dake son tsoma baki kan batun Taiwan, da kuma tsoma baki kan harkokin cikin gidan kasar Sin, kuma irin wadannan sassa ba za su cimma nasara ba. (Mai Fassara: Maryam Yang)

 

Wang yi
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Wang yi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Gwamnatin Ƙasar Gabon Ta Ɗage Dakatarwar Da Ta Yi Wa Aubameyang

Gwamnatin Ƙasar Gabon Ta Ɗage Dakatarwar Da Ta Yi Wa Aubameyang

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.