Gwamnatin kasar Gabon ta dage takunkumin da ta sanya wa tawagar kasar da kuma dan wasan gaba kuma kyaftin din tawagar Pierre-Emerick Aubameyang, Gwamnatin ta dakatar da ayyukan tawagar kwallon kafa ta kasar bayan sun fice daga gasar cin kofin Afirka na shekarar 2025.
Gabon ta kare a matsayi na karshe a rukunin F inda ta buga wasanni 3 na rukuni ba tareda da samun maki ko daya ba, hakazalika an zurawa kasar kwallaye 7 yayinda ta jefa 3, Ministan wasanni na wancan lokacin Simplice-Desire Mamboula ya kira yanayin da tawagar ta samu kan ta a matsayin “abin kunya”.
Mamboula ya sanar da dakatar da tawagar, tareda korar koci Thierry Mouyouma da kuma korar tsohon dan wasan Arsenal da Chelsea Aubameyang da kyaftin Bruno Ecuele Manga daga tawagar wadda ake yiwa lakabi da Panthers a ranar 1 ga watan Janairu.
Amma yanzu sabon ministan wasanni na Gabon, Paul Ulrich Kessany, ya dage takunkumin wanda idan ba’a dakatar ba ka iya janyowa hukumar kwallon kafa ta Gabon (FEGAFOOT) kora daga hukumar kwallon kafa ta Duniya (FIFA) idan dakatarwar ta cigaba da kasancewa har zuwa ranar Litinin, FIFA na daukar tsatstsauran matakin akan tsoma bakin gwamnatoci a harkar kwallon kafa a halin yanzu.















Discussion about this post