Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya yi hira da sakataren harkokin waje na Amurka Marco Rubio ta wayar tarho a jiya 17 ga watan Satumba. Bangarorin biyu sun tattauna sosai kan cudanya tsakanin manyan shugabannin kasashen biyu.
Wang Yi ya ce, dangantakar Sin da Amurka na tafiya yadda ya kamata bisa manyan tsare-tsare da shugabannin kasashen biyu suka tsara a baya-baya nan, matakin da ya dace da bukatu da fatan al’ummar duniya.
Wang Yi, ya jaddada cewa, tuntubar shugabannin kasashensu muhimmin karfi ne na tabbatar da huldar Sin da Amurka, kuma ya kamata bangarorin biyu su share fagen mu’ammalar shugabannin kasashen a karo mai zuwa bisa tushen daidaito, girmama juna da cin moriya tare, kana da karfafa mu’ammala da ingiza hadin gwiwa da daidaita bambancin ra’ayi da mutunta muradunsu, ta yadda za a samar da sako mai kyau na kokarin ingiza huldar kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare, da karfafa zaman lafiya da ci gaban duniya.
Ban da wannan kuma, bangarorin biyu sun kuma yi musayar ra’ayi kan halin da ake ciki a yankin Gabas Ta Tsakiya da sauransu.(Amina Xu)
Wang Yi Ya Yi Hira Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio Ta Wayar TarhoMinistan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya yi hira da sakataren harkokin waje na Amurka Marco Rubio ta wayar tarho a jiya 17 ga watan Satumba. Bangarorin biyu sun tattauna sosai kan cudanya tsakanin manyan shugabannin kasashen biyu.Wang Yi ya ce, dangantakar Sin da Amurka na tafiya yadda ya kamata bisa manyan tsare-tsare da shugabannin kasashen biyu suka tsara a baya-baya nan, matakin da ya dace da bukatu da fatan al’ummar duniya. Wang Yi, ya jaddada cewa, tuntubar shugabannin kasashensu muhimmin karfi ne na tabbatar da huldar Sin da Amurka, kuma ya kamata bangarorin biyu su share fagen mu’ammalar shugabannin kasashen a karo mai zuwa bisa tushen daidaito, girmama juna da cin moriya tare, kana da karfafa mu’ammala da ingiza hadin gwiwa da daidaita bambancin ra’ayi da mutunta muradunsu, ta yadda za a samar da sako mai kyau na kokarin ingiza huldar kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare, da karfafa zaman lafiya da ci gaban duniya.Ban da wannan kuma, bangarorin biyu sun kuma yi musayar ra’ayi kan halin da ake ciki a yankin Gabas Ta Tsakiya da sauransu.(Amina Xu)














