A yau Asabar, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya aike da sakon taya murna ga shugaban Angola Joao Lourenco, wanda shi ne shugaban karba-karba na Tarayyar Afrika, da Mahamoud Youssouf, shugaban hukumar kula da AU, inda ya taya kasashe da jama’ar Afrika murna game da taron AU na 39.
Shugaba Xi Jinping ya bayyana cewa, yanzu haka duniya na fuskantar sauye-sauye cikin sauri irin wadanda aka dade ba a gani ba, kuma kasashe masu tasowa na samun karin tasiri. Ya ce cikin shekarar da ta gabata, AU ta hada kan kasashen Afrika tare da jagorantarsu wajen inganta dunkulewar nahiyar da kare hakkoki da muradunsu da ci gaba da inganta matsayi da tasirin nahiyar a duniya.
Shugaban na Sin ya nanata cewa, yayin da ake fuskantar yanayi mai sarkakiya a duniya, kasar Sin za ta jajirce wajen kare zaman lafiya da inganta ci gaban duniya, da inganta gina duniya mai makoma ta bai daya ga bil adama. Haka kuma, Sin za ta aiwatar da matakanta na soke haraji ga kasashe 53 dake da huldar diplomasiyya da ita daga ranar 1 ga watan Mayun 2026. Haka kuma, za ta ci gaba da rattaba hannu kan yarjeniyoyin hadin gwiwar raya tattalin arziki na bai daya da kara fadada shigar kayayyakin Afrika kasar Sin bisa daukaka hanyar shigar kayayyakin da ba sa bukatar biyan haraji da sauran matakai.
Ya ce wannan sabon mataki ne na Sin na fadada bude kofarta, wanda tabbas zai samar da sabbin damarmaki wajen raya nahiyar Afrika da cimma burin bai daya na zamanantar da Sin da Afrika. (Mai fassara: FMM)















Discussion about this post