Da yake albashinsu baya isarsu su samu damar sayen isasshen abinci, biya kudin haya da kuam kudin zirga- zirgar, shi asa dabi’ar koyarwa bayan an tashi daga makaranta ya kasance wani sabon babi ga Malaman makaranta saboda su samu damar r da zata taimaka masu wajen tafiyar da rayuwarsu da iyalai a cikin halin matsin tattalin arziki.
Irin wannan a shekarun baya bai zama dole ba amma yanzu abin ya kasance wata hanya ce da su Malaman suke amfani da ita domin su samu dama ta tafiyar da rayuwarsu musamman ma idan aka yi la’akarin da irin cikin kuncin wahalhalun da ake fuskanta saboda irin albashin da ke basu ba wani abu yake isarsu yi ba, ba ma irin yadda makarantu da yawa suke biya, kamar makarantu masu zaman kansu.
- An Gabatar Da Bikin Share Fagen Shirin Talibijin Na Murnar Sabuwar Shekarar Sinawa A Masar
- Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Samar Da Kundin Amfani Da Takin Zamani
A fadin tarayyar Nijeriya, yadda kullun rayuwa take kara yin tsada ya sa ma’aikata suka kara shiga wani hali na ni ‘yasu, sai dai kuma bain ya fi damuwar Malaman makaranta.
Tsadar rayuwa, karuwar kudaden zirga- zirga, kudaden haya ma sun karu, ga kuma karuwar farashin kayan abinci, duk hakan ya sa duk yawan albashin da ma’aikaci yake amsa abin sai dai kawai ayi sha’ani wai an cuci na Kauye.
Ga yawancin Malaman makaranta, musamman masu aiki a makarantu masu zaman kansu, albashin d a ake nasu kowane wata baya isar su biyan bukatun da suke dole sai an san yadda za’a tafiyar da su.
Ya yin da tattalin arzikin Nijeriya yake kara samun matsaloli, sai aikin koyarwa na wucin gadi bayan an tashi daga makaranta sai abin a saukake ya kasance wata kafa ce ta tsira da mutunci ga wasu Malaman makaranta, musamman ma masu zama a birane kamar Abuja, Legas da kuma sauransu.
A cikin biranen,yadda tsadar rayuwar take ta kara tsada, irin koyarwar ta bayab an tashi daga makaranta tana taimakawa su Malaman ,makaranta da albashin nasu bai taka kara ya karaya ba,idan aka yila’akari da tasadar rayuwa saboda tabarbarewar tattalin arziki.
Yayin da malarantu ‘yan kadan ne suke biyan albashi mai tsoka, yawancinsu suna biyan albashin da babu irin bukatun da zai iya biya na su Malaman makarantar.
Alal misali a Abuja,albashin makarantu masu zaman kansu ya fara ne daga ne daga Naiar 30,000 zuwa kusan Naiar 500,000, wannan kuma ya danganta ne ga yadda makarantar ta ke da kuma wanda ya mallake ta.
Sai dai kuma,makarantun da suke biyan tsakanin Naiar 200,000 Naira 500,000 kadan ne, lamarin da ya bar yawancin Malaman makaranta suna samun albashin da bai isarsu zama a cikin birnin cikin dadin rayuwa.
Tunda suna fuskantar wadannan matsalolin da suka shafi tattalin arziki da tsadar rayuwa, yawancin Malaman makaranta yanzu sun zama Malaman koyarwa na wucin gadi suna koyar da wasu darussa bayan sun tashi daga makaranta, domin hakan zai taimaka masu wajen karuwar kudaden shiga.Yawancin Malaman da suka tattauna da LEADERSHIP sun bayyana cewa yanzu suna samun kudi sosai daga daga darussan da suke koyarwa bayan sun tashi daga makaranta.Gare su, koyar da darussan da suke zuwa gida ya zame wata dama da ta zama dole saboda karuwar samun kudi.
Wasu Malaman duk da suke ganin samun kudi ya zo. Sai dai suna daukar lokaci mai tsawo na awoyi wajen aiki ga kuma gajiya. Yawancinsu suna tashi aiki ne tsakanni karfe 4.00 zuwa 5.00 na yamma, daga can ne kuma suke zuwa gidajen da suke koyar da darussa gida lamarin da zai kai su ga tashi da dare wani lokaci kwarai.
Saura kuma suna yin amfani ne da lokacin hutunsu na karshen mako suna zuwa daga wannan gida zuwa wancan suna koyar da yaran da Iyayensu za su iya biyan kudin.
Wasu Malamai sun ce matsalolin rayuwa ne suka sa suka ajiye aikin koyarwa domin su samu maida hankalinsu kan lamarin koyarwa na darussan gida kadai, lamarin da suke ganin sun fi samun kudi ga shi kuma sune tsara yadda za su tafiyar da lokacinsu.
Wani Malami a Abuja, da ya bayyana sunan sa Moses, ya ce yanzu yana aiki ne a matsayin Malamin da yake koyarwa da darussa a gidas,yana amsar tsakanin Naira 50,000 da Naira 100,000 ga duk mutumin da ya koyar da dansa, wannan kuma abin ya dogara ne kan irin darasin da ya koyar da kuma ko awa nawa ya yi. Ya ce dalilin da yasa ya bara lamarin koyarwa a aji lamarin tattalin arziki ne kawai.
Ya ce “Wurin da yake aiki a baya ana biyansa Naira 80,000 kowane wata,kuma yana yin ayyuka masu yawa.Yana koyar d a azuzuwa masu yawa,hakanan ma akwai darussa masu yawa, amma duk da haka da kyar da jibing goshi ya ke kai labari. Ya ce yanzu da darussa da yake zuwa gida yana koyawa,yana samun fiye da Naira 200,000, ga shi kuma yana samun lokacin hutawa.”















Discussion about this post