A kwanakin baya, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya amsa wasikar malamai da dalibai, na tawagar mu’amalar matasa ta kasar Amurka, wadda ta hada da na kwalejin koyar da ilmi ga matukan jiragen sama dake Miami, da jami’ar Florida, da kwalejin Miami-Dade ta jihar Floridan kasar Amurka.
A cikin wasikar, shugaba Xi Jinping ya bayyana cewa, yana jin dadin ganin yadda malamai da dalibai na tawagar su yi farin ciki da ziyararsu a kasar Sin, ya kuma lura da yadda suka bayyana sha’awarsu ga al’adun kasar Sin.
Xi, ya yi nuni da cewa, raya dangantaka tsakanin Sin da Amurka, na da nasaba da jama’arsu, kuma makomar dangantakar ya ta’allaka ga matasa. Bayan kaddamar da kiran gayyata ga matasan kasar Amurka dubu 50 zuwa kasar Sin, domin yin mu’amala da karatu a cikin shekaru 5, an riga an samu halartar matasan Amurkan fiye da dubu 40 zuwa kasar Sin, wadanda suka kara fahimtar hakikanin kasar Sin, da kasancewa wata gadar sada zumunta a tsakanin kasashen biyu. Wannan ya shaida cewa, yin mu’amala, da hadin gwiwa, da sada zumunta ya dace da burin jama’ar kasar Sin da Amurka.
A kwanakin baya, tawagar mu’amalar matasa ta kasar Amurka, ta aikewa shugaban kasar Sin Xi Jinping wata wasika, wadda a ciki aka waiwayi ziyararta a kasar Sin a watan Oktoban shekarar 2025, tare da nuna godiya ga gayyatar matasan kasar Amurka da shugaba Xi ya yi, wadda ta samar da damar fahimtar juna a tsakanin matasan kasashen biyu. (Zainab Zhang)















Discussion about this post