Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya bayar da muhimmin umarni na yin dukkan mai yiwuwa wajen ceto mutanen da suka bata, da kuma kulawa da wadanda suka jikkata, sanadiyyar fashewar gas a wani wurin hakar kwal a lardin Shanxi da ke arewacin kasar.
Xi Jinping wanda kuma shi ne sakatare janar na kwamitin kolin JKS kuma shugaban hukumar koli ta soji, ya bukaci a gudanar da ayyukan ceto bisa tsari da kwarewa kuma, a tafiyar da harkoki masu ruwa da tsaki yadda ya kamata, bayan aukuwar hatsarin.
Ya kuma bukaci a gaggauta gudanar da binciken musababbin hatsarin, yana mai nanata cewa dole ne a hukunta wadanda ke da alhaki.
Fashewar gas din ta auku ne a karkashin kasa a wurin hakar kwal na Liushenyu da ke gundumar Qinyuan, da misalin karfe 7:29 na yammacin jiya Juma’a, lamarin da ya rusta da mutane.
Ya kara da cewa, ya zama wajibi hukumomi daban daban a duk fadin kasar su dauki darasi daga aukuwar lamarin, su kuma kara sa ido sosai kan tabbatar da aminci da tsaron rayuka a wuraren aiki, da kara kokarin ganowa da kawar da barazanar hadura domin kare aukuwar manyan ibtila’i. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post