Yau Talata da safe, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugaban kasar Myanmar Min Aung Hlaing, a babban dakin taron jama’a dake birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.
A yayin ganawarsu, Xi Jinping ya ce, a bana aka fara aiwatar da shirin shekaru biyar-biyar na bunkasa tattalin arziki da zamantakewar kasar Sin na 15, kuma kasar Sin tana son yin mu’amala da kasar Myanmar kan fasahohin neman ci gaban kasa, tare da samun fahimtar juna kan harkokin siyasa, da tallafa wa juna kan aikin neman bunkasuwa, da taimaka wa juna kan aikin kare tsaron kasa, da yin musaya kan harkokin al’adu, ta yadda za a kafa makomar kasashen Sin da Myanmar ta bai daya, tare da ba da karin tallafi ga jama’ar kasashen biyu.
Xi ya kuma jaddada cewa, ya kamata Sin da Myanmar su duba yanayin duniya da idon basira, tare da karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu. Ya ce kasar Sin tana goyon bayan bangarorin kasar Myanmar wajen warware sabanin dake tsakaninsu ta hanyar shawarwari, ta yadda za a shimfida zaman lafiya na dindindin a arewacin kasar, lamarin da zai dace da moriyar jama’a da kasar ta Myanmar.
A nasa bangare kuma, Min Aung Hlaing ya ce, kasarsa na fatan inganta hadin gwiwar dake tsakaninta da kasar Sin bisa dukkan fannoni, domin kafa hanyar hadin gwiwar tattalin arziki a tsakanin Sin da Myanmar, da daga matsayin zuba jari a bangaren cinikayya.
Bayan ganawarsu, shugabannin kasashen biyu sun halarci bikin sa hannu kan takardun hadin gwiwa dake shafar aikin zirga-zirga, da ababen more rayuwa da dai sauransu.
Kafin ganawarsu kuma, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kaddamar da bikin maraba da zuwan shugaban na kasar Myanmar Min Aung Hlaing kasar Sin, a babban dakin taron jama’a.
Bisa gayyatar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi masa, shugaban kasar Myanmar Min Aung Hlaing ya fara yin ziyarar aiki a kasar Sin a tsakanin ranakun 15 zuwa 19 ga watan nan na Yuni. (Mai Fassara: Maryam Yang)















Discussion about this post