A yau Alhamis 5 ga wannan wata, babban sakataren kwamitin tsakiya na jam’iyyar Kwaminis ta Sin, kuma shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci taron tattaunawa da tawagar wakilan jama’a ta lardin Jiangsu, mahalartar zama na hudu na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin wato NPC karo na 14.
A yayin taron tattaunawar, Xi Jinping ya jaddada cewa, ya kamata a kara maida hankali ga yin bincike kan sabon yanayi na daidaita sabbin matsaloli a lardin Jiangsu mai ci gaban tattalin arziki a kasar.
Xi Jinping ya yi nuni da cewa, raya sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko yana da muhimmanci wajen sa kaimi ga samun bunkasuwa mai inganci da kara karfin tattalin arzikin kasar. Sai dai ya kamata a sa kaimi ga horar da kwararru a fannin kimiyya da fasaha, da yin kokari wajen samun sabon ci gaban kirkire-kirkire a fannin kimiyya da fasaha, da hadin kan yin kirkire-kirkire da sha’ani da kwararru, da sa kaimi ga yin amfani da nasarorin kimiyya da fasaha yadda ya kamata, da kuma inganta sha’ani na gargajiya, da sabbi, da kuma na nan gaba baki daya. (Zainab Zhang)















Discussion about this post