Fitaccen mawaƙin Kudancin Nijeriya, Davido, ya caccaki mawaƙin siyasa, Dauda Kahutu Rarara, inda ya zarge shi da fifita siyasa a kan gaskiyar halin rashin tsaron da Nijeriya ke ciki.
Taƙaddamar ta samo asali ne bayan Davido ya bayyana a bikin buɗe gasar Kofin Duniya ta 2026 da aka gudanar a Los Angeles, inda ya sanya wata riga da aka rubuta “Bring Them Home” (A Dawo Da Su Gida), tare da sunayen ɗalibai da malamai sama da 40 da aka sace a Jihar Oyo.
Rarara ya soki matakin, yana mai cewa bai dace a riƙa bayyana matsalolin tsaron Nijeriya a idon duniya ba.
A cewarsa, hakan na iya ɓata sunan ƙasar tare da jefa ta cikin mummunan hali a idon ƙasashen duniya.
Ya kuma yi zargin cewa matakin Davido na iya kasancewa yana da nasaba da siyasa.
Da farko, Davido ya mayar masa da martani cikin raha a shafinsa na sada zumunta, amma daga baya ya fitar da cikakken bayani inda ya ce bai kamata ‘yan Nijeriya su yi shiru kan matsalar rashin tsaro da ke addabar ƙasar ba.
Mawakin ya ce kishin ƙasa na gaskiya shi ne a yi magana kan matsalolin da ke damun al’umma maimakon kare muradun siyasa.
Ya kuma zargi wasu da fifita buƙatunsu na siyasa da na ƙashin kansu a kan muradun ƙasa da walwalar jama’a.
“Ya kamata kowane ɗan Nijeriya ya yi magana kan matsalar rashin tsaro,” in ji Davido.
“Ku daina fifita siyasa a kan gaskiya, ku sanya Nijeriya a gaba a cikin duk abin da kuke yi.”
Ce-ce-ku-cen ya jawo muhawara a kafafen sada zumunta, inda magoya bayan ɓangarorin biyu ke ganin ko bayyana matsalar rashin tsaro a duniya zai taimaka wajen jawo hankali ga matsalar ko kuwa zai ɓata sunan Nijeriya.














Discussion about this post