Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya aike da sakon taya murna ga Yoweri Kaguta Museveni, bisa nasarar lashe babban zaben kasarsa na baya bayan nan, wanda hakan ya ba shi damar ci gaba da rike ragamar shugabancin kasar Uganda.
A cikin sakon na sa, shugaba Xi ya bayyana cewa, kasashen Sin da Uganda, suna da kyakkyawar alaka ta gargajiya. A cikin ’yan shekarun nan, bangarorin biyu sun goyi bayan juna sosai, kan batutuwan da suka shafi manyan muradunsu da kuma manyan abubuwan dake damunsu, kana an cimma sakamako mai kyau a hadin gwiwarsu ta fannoni daban daban.
Shugaban na Sin ya kara da cewa, shugaba Museveni tsohon abokin al’ummar Sin ne, kuma ya dade yana himmatuwa wajen habaka dangantakar kasashen biyu, matakin da Sin ta yabawa matuka.
Ya ce “Ina dora muhimmanci ga ci gaban dangantakar Sin da Uganda, kuma ina fatan yin aiki tare da shugaba Museveni, don aiwatar da sakamakon da aka samu a gun taron kolin birnin Beijing, na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka, da zurfafa ci gaban dangantakar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Uganda, da kuma amfanar da al’ummomin kasashen biyu. (Safiyah Ma)















Discussion about this post