A yau Jumma’a ne aka gudanar da dandalin kasa da kasa na tattauna shekarar zaman lafiya da aminci, a birnin Ashgabat dake Turkmenistan. Kuma shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aike da wasikar taya murna ga taron.
Cikin wasikar tasa Xi Jinping, ya jaddada cewa a halin yanzu duniya na fuskantar kalubale da dama, da kuma rikice-rikice, da takaddama marar iyaka. Ya ce sama da ko wane lokaci a baya, a yanzu duniya ta fi kira ga zaman lafiya da aminci. Xi ya kara da cewa, kamata ya yi dukkan kasashen duniya su bi ka’idar tattaunawa game da harkokin duniya tare, da kiyaye tsarin kasa da kasa tare, da kuma raba fa’idodin da aka samu daga shugabanci tare.
Xi Jinping ya bayyana cewa, kwanan nan ya gabatar da shawarar tsarin shugabancin duniya, wadda za ta samar da mafita ta kasar Sin, don gyarawa, da inganta tsarin shugabancin duniya. Kazalika, Sin na fatan yin aiki tare da dukkan kasashe, don kare zaman lafiyar duniya, da inganta ci gaba tare, da kuma kyautata gina al’umma mai makomar bai daya ga daukacin bil’adama. (Safiyah Ma)














