A yau Laraba ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya bayyana bukatar daidaita tsare-tsaren samar da ci gaba, da fifita matakan hade ababen more rayuwa tsakanin kasarsa da Vietnam.
Shugaba Xi, wanda kuma shi ne babban sakataren kwamitin kolin JKS, ya yi kiran ne yayin da yake zantawa da sakataren kwamitin kolin jam’iyyar Kwaminis ta Vietnam, kana shugaban kasar To Lam, wanda ke ziyarar aiki yanzu haka a kasar Sin.
Xi, ya kuma kara da yin kira ga sassan biyu, da su karfafa hadin gwiwa a sabbin fannoni, irinsu fasahar kirkirarriyar basira, da kirar sassan hada laturoni na semiconductors, da sauran sassan harhada tsarin aikin intanet, yana mai cewa, kasuwannin Sin na maraba da karin hajoji masu inganci na kasar Vietnam. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post