Shugaban kasar Sin, Xi Jinping, ya yi kira da a dauki kwararan matakai domin zurfafa zamanantar da harkokin aikin gona da yankunan karkara.
Xi, wanda har ila yau shi ne babban sakataren kwamitin tsakiya na JKS, kuma shugaban hukumar soji ta tsakiya, ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar duba aiki da ya kai birnin Dezhou na lardin Shandong da ke gabashin kasar Sin a yau Laraba.
Ya bayyana cewa ya kamata a kara kaimi wajen inganta cikakken karfin samar da amfanin gona da kuma ingancinsa, da tabbatar da wadatacciyar samar da muhimman kayayyakin gona kamar hatsi, da habaka gina yankunan karkara masu dadin zama, da gudanar da kasuwanci cikin sauki kana masu kyawun gani bisa yanayin kowane yanki.
Haka kuma, ya ce ya kamata a jagoranci manoma wajen samar wa kansu rayuwa mafi inganci ta hanyar nuna kwazo da kuma hikima. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)














