A yau Asabar ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi musayar sakon taya murna da takwaransa na Masar Abdel-Fattah al-Sisi, dangane da cika shekaru 70 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Masar.Cikin sakonsa, shugaba Xi ya ce cikin shekaru 70 da suka gabata, duk da sauye-sauye da aka fuskanta a harkokin kasa da kasa da na shiyyoyi, Sin da Masar sun wanzar da martaba juna, da daukar junansu daidai wa daida, sun amincewa juna, tare da taimakawa juna a dukkanin lokutan bukata.
Shugaban na Sin ya kara da cewa, alakar Sin da Masar ta zamo misali na kyakkyawan kawance, da goyon baya, da hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa, kana hakan ya zamo muhimmin jigo na gamammen hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Larabawa, da tsakanin Sin da nahiyar Afirka.
Daga nan sai shugaba Xi ya bayyana irin muhimmanci da yake dorawa ga bunkasar alakar Sin da Masar, yana mai shan alwashin aiki tare da shugaba Al-Sisi, don mayar da wannan gaba ta cika shekaru 70 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin sassan biyu wani sabon mafari, tare da ingiza kawancen gargajiya, da karfafa musaya, da hadin gwiwarsu a sassa daban daban, kana da bunkasa ci gaban alakar Sin da Masar, karkashin manyan tsare-tsare, da daidaito mai karfi, don rayawa, da bunkasa tasirinsu a matakin kasa da kasa. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post