Am bayyana cewa a sakamakon rikice-rikicen da ke faruwa a tsakanin waɗansu ƙasashen duniya shi ne ya ƙara dagula rayuwar al’umma tare da sauran harkokin kasuwanci a nan gida Nijeriya da waɗansu ƙasashen duniya baki ɗaya, wani babban ɗan kasuwar ƴan gwagwan a Legas mai suna Alhaji Ibirahim Abdullahi Ɗansoja da ke gidan kwali unguwar Ojota wanda ya kasance shi ne sarkin ƴan gwagwan na jihohi goma sha bakwai a Nijeriya shi ne ya tabbatar da hakan a lokacin da yake zantawa da waɗansu wakilan kafofin yaɗa labarai dangane da al’amarin.
Alhaji Ibirahim Abdullahi Ɗansoja ya ci gaba da cewa, rikice-rikice na ƙasashen ƙetare ya ba da gudummawa a wajen dagula rayuwar al’umma tare da taɓarɓarewar harkokin kasuwanci a Nijeriya, ya ci gaba da cewa wannan al’amari na tashin farashin man fetur a Nijeriya ya shafi sana’ar su ta kasuwancin gwagwan da sauran sana’oi a Nijeriya.
Ya ƙara da cewa a yanzu haka wahalhalun da suke dama dasu kafin kai kaya kamfani ya tashi daga kashi hamsin ya koma kashi ɗari da a shirin domin a wannan lokacin suna shatar mota mai kwasar masu kayan gwagwan zuwa kamfanonin da ake sarrafasu a kan dubu ɗari biyu amma saboda wannan matsalar ta ƙarin farashin man fetur suna shatar mota zuwa kamfanin sarrafa kayan a kan naira dubu ɗari uku da hamsin, ya ce a kan haka yake ƙara shawartar Gwamnatin Nijeriya da ta taimaka ta nemo wa ƴan kasuwar Nijeriya waɗansu hanyoyi da suka dace waɗanda za su samu sauƙin wannan al’amari.
Ya kuma nuna rashin jin daɗinsa dangane da yadda ma’aikata ke damun su a wuraren da suke tara kayan su na gwagwan kafin kwashewa zuwa kamfanin sarrafawa, ya ce ma’aikatan suna matuƙar damun su ƙwarai da haske a wajen tambayar su takardar shaidar inda suka sayi kaya wato rasit kenan.
Sarkin na ƴan gwagwan Alhaji ibirshim Abdullahi Ɗansoja ya ci gaba da cewa kowa ya sani cewar kayan gwagwan kaya ne waɗanda ya riga ya lalace ba shi da wani amfani haka suke sayan sa domin mayar dashi kamfani a sarrafa shi ya dawo yadda ake buƙata amma duk da hakan ma’aikatan basu kulawa da hakan suna yawan takura masu a wuraren da suke tara kayan gwagwan a kowanne lokaci suna zuwa suna bincikar su takardar rasit, in ji shi.
Ya yi fatan Gwamnatin Jihar Legas za ta tsawata wa ma’aikatan dangane da wannan alamari, ya kuma yi addu’ar Allah ya dawo da Alhazanmu gida lafiya.















Discussion about this post