Kasashen duniya suna ci gaba da mayar da hankali sosai kan ziyarar da shugaban Amurka Donald Trump ya gudanar a kasar Sin daga ranar 13 zuwa 15 ga watan nan na Mayu. A yayin ziyarar, shugabannin kasashen Sin da Amurka sun gudanar da babbar ganawa, inda suka amince cewa, matakin kafa “dangantaka mai dorewa, da amfani, bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Amurka”, zai zama mafi mahimmanci ta fannin siyasa.
Ganawar ta wannan karo ta kunshi tattaunawa a hukumance, da liyafar maraba, da kuma kananan ayyuka na musayar ra’ayoyi da ziyara. Shugabannin kasashen biyu sun yi mu’amala ta kusan sa’o’i tara, sun habaka fahimtar juna, da zurfafa amincewa da juna, da bunkasa hadin gwiwa mai amfani, da kuma inganta walwalar jama’ar kasashen biyu.
Hakan ya kuma nuna wa duniya cewa, a ko da yaushe dangantakar diplomasiyya tsakanin shugabannin kasashen Sin da Amurka ita ce “tauraruwa mai ba da jagoranci” ga dangantakar Sin da Amurka.
Bugu da kari, yayin ganawar shugabannin biyu, Sin ta sake nanata aniyarta ta maraba da Amurka, a fannin karfafa hadin gwiwa mai amfanar juna tare da Sin.
Shugaba Trump, ya kuma bayyana cewa zai karfafa gwiwar ’yan kasuwar Amurka dake tare da shi, wajen fadada hadin gwiwa da Sin.
Jama’a na ganin cewa Sin da Amurka za su ci gaba da fadada jerin hadin gwiwa, da rage jerin batutuwan sabani, da habaka hadin gwiwar tattalin arziki da ciniki mai amfani, da kuma samar da karin damarmaki na ci gaba ga bangarorin biyu. (Safiyah Ma)















Discussion about this post