ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Kasa Da Kasa Su Hada Hannu Su Kare Wayewar Kan Duniya Daga Masu Yunkurin Mayar Da Hannun Agogo Baya

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Kasa

Yayin da yanayin ya dau zafi a yankin Gabas ta Tsakiya da ma duniya baki daya, saboda mummunan matakin Amurka da Isra’ila na farwa Iran yayin da ake tsaka da tattaunawa a tsakanin Iran da Amurka, kamar kullum, kasar Sin ta bayyana matsayarta a matsayinta na wadda ta san ya kamata. Kuma a ganina batutuwan da ta bayyana, su ne hanyoyin samun zaman lafiya da karewa da tabbatar da cikakken ’yancin kasashen duniya.

A jiya Lahadi, yayin tattaunawa ta wayar tarho tsakanin ministan harkokin wajen Sin Wang Yi da takwaransa na Rasha, Sergei Lavrov bisa bukatar Lavrov din, ministan na kasar Sin ya fayyace matsayar kasarsa dangane da batun.

Kamar yadda ya fada, ya kamata a gaggauta dakatar da kai hare-hare domin kandagarkin bazuwar rikicin. Duniya na cikin yanayi na tashin hankali. Har yanzu ana fama da rikice-rikice a sassan daban-daban daga na Rasha da Ukraine, zuwa na Sudan da yankin Gaza, inda al’ummomin duniya da ba su ji ba su gani ba, suke dandana kudarsu saboda mummunan tasirinsu. Shin wannan kadai bai isa ya sa Amurka da Isra’ila su sassauta daga amfani da karfi fa? Shin wannan yunkuri na wanzar da zaman lafiya ko kuwa na kara hargitsa duniya?

ADVERTISEMENT

A wannan sabon zamanin da ake ciki da tarin kalubalen da dan Adam ke fuskanta, bai kamata a ce ana nuna karfi kamar zamanin mulkin mallaka da babu ’yantattun kasashe da dokokin kasa da kasa ko hukumomi masu shiga tsakani ba.

Abu na biyu da Wang Yi ya bayyana shi ne, gaggauta komawa teburin sulhu.

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Mun ga yadda dukkan yake-yake da rikice-rikicen dake wakana ke komawa teburin sulhu bayan gwabza fada, lamarin dake nuna cewa, amfani da karfi ba ya haifar da da mai ido. Yanayi da al’adun kasashe sun bambanta, don haka dole a samu sabanin ra’ayi tsakanin bangarori daban-daban, amma a matsayin mutane wadanda suka mallaki hankali, kamata ya yi a rika amfani da hankali da hangen nesa, a tattauna don lalubo hanyoyin cimma yarjejeniya da hakuri da wasu batutuwa domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali. Diplomasiyya ta fi taka rawa a dangantakar kasa da kasa sama da fito na fito da raini da amfani da karfi.

Batu na 3 da ministan na Sin ya tabo shi ne, kasa da kasa su hada kai wajen adawa da yadda ake gaban kai wajen daukar matakai. Hakika yin gaban kai wajen daukar matakai, sam bai dace da zamanin wayewar kai da ilimi ba. Wannan salo ne na rashin wayewa, kuma ya zama wajibi kasa da kasa su hadu su yi magana da murya guda don kaucewa mayar da hannu agogo baya na ci gaban da dan adam ya samu. Muddun aka gaza yin hakan, to babu wanda zai tsira.

Hakika a matsayinta na babbar kasa da kullum take nuna hangen nesa da sanin ya kamata, kasar Sin ta gabatar da hanyoyi masu dacewa na tabbatar da zaman lafiya a duniya. Sai dai, ita kadai ba za ta iya ba. Fatan ita ce, kasa da kasa su yi nazari, su kuma yi abun da ya kamata. (Fa’iza Mustapha)

Kasa
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30
Kasa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka
  • Sulaiman
    Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen
  • Sulaiman
    Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya
  • Sulaiman
    2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

MASU ALAKA

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?
Daga Birnin Sin

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Next Post
Matatar Dangote Ta Ƙara Farashin Fetur, Ta Dakatar Da Lodi

Matatar Dangote Ta Ƙara Farashin Fetur, Ta Dakatar Da Lodi

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Za A Ci ’Yan Siyasa Masu Kalaman Ɓatanci Tarar Miliyan 10 Da Ɗaurin Watanni 12 — INEC

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026  Mrs Zubaida Umar

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026 Mrs Zubaida Umar

September 11, 2026
Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

September 11, 2026
Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

September 11, 2026
Sanata yari

Gwarzon Ɗan Siyasa Na Shekarar 2026 Sanata Abdul’Aziz Abubakar Yari

September 11, 2026
Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.