ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Kasa Da Kasa Su Hada Hannu Su Kare Wayewar Kan Duniya Daga Masu Yunkurin Mayar Da Hannun Agogo Baya

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Kasa

Yayin da yanayin ya dau zafi a yankin Gabas ta Tsakiya da ma duniya baki daya, saboda mummunan matakin Amurka da Isra’ila na farwa Iran yayin da ake tsaka da tattaunawa a tsakanin Iran da Amurka, kamar kullum, kasar Sin ta bayyana matsayarta a matsayinta na wadda ta san ya kamata. Kuma a ganina batutuwan da ta bayyana, su ne hanyoyin samun zaman lafiya da karewa da tabbatar da cikakken ’yancin kasashen duniya.

A jiya Lahadi, yayin tattaunawa ta wayar tarho tsakanin ministan harkokin wajen Sin Wang Yi da takwaransa na Rasha, Sergei Lavrov bisa bukatar Lavrov din, ministan na kasar Sin ya fayyace matsayar kasarsa dangane da batun.

Kamar yadda ya fada, ya kamata a gaggauta dakatar da kai hare-hare domin kandagarkin bazuwar rikicin. Duniya na cikin yanayi na tashin hankali. Har yanzu ana fama da rikice-rikice a sassan daban-daban daga na Rasha da Ukraine, zuwa na Sudan da yankin Gaza, inda al’ummomin duniya da ba su ji ba su gani ba, suke dandana kudarsu saboda mummunan tasirinsu. Shin wannan kadai bai isa ya sa Amurka da Isra’ila su sassauta daga amfani da karfi fa? Shin wannan yunkuri na wanzar da zaman lafiya ko kuwa na kara hargitsa duniya?

ADVERTISEMENT

A wannan sabon zamanin da ake ciki da tarin kalubalen da dan Adam ke fuskanta, bai kamata a ce ana nuna karfi kamar zamanin mulkin mallaka da babu ’yantattun kasashe da dokokin kasa da kasa ko hukumomi masu shiga tsakani ba.

Abu na biyu da Wang Yi ya bayyana shi ne, gaggauta komawa teburin sulhu.

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Mun ga yadda dukkan yake-yake da rikice-rikicen dake wakana ke komawa teburin sulhu bayan gwabza fada, lamarin dake nuna cewa, amfani da karfi ba ya haifar da da mai ido. Yanayi da al’adun kasashe sun bambanta, don haka dole a samu sabanin ra’ayi tsakanin bangarori daban-daban, amma a matsayin mutane wadanda suka mallaki hankali, kamata ya yi a rika amfani da hankali da hangen nesa, a tattauna don lalubo hanyoyin cimma yarjejeniya da hakuri da wasu batutuwa domin samun zaman lafiya da kwanciyar hankali. Diplomasiyya ta fi taka rawa a dangantakar kasa da kasa sama da fito na fito da raini da amfani da karfi.

Batu na 3 da ministan na Sin ya tabo shi ne, kasa da kasa su hada kai wajen adawa da yadda ake gaban kai wajen daukar matakai. Hakika yin gaban kai wajen daukar matakai, sam bai dace da zamanin wayewar kai da ilimi ba. Wannan salo ne na rashin wayewa, kuma ya zama wajibi kasa da kasa su hadu su yi magana da murya guda don kaucewa mayar da hannu agogo baya na ci gaban da dan adam ya samu. Muddun aka gaza yin hakan, to babu wanda zai tsira.

Hakika a matsayinta na babbar kasa da kullum take nuna hangen nesa da sanin ya kamata, kasar Sin ta gabatar da hanyoyi masu dacewa na tabbatar da zaman lafiya a duniya. Sai dai, ita kadai ba za ta iya ba. Fatan ita ce, kasa da kasa su yi nazari, su kuma yi abun da ya kamata. (Fa’iza Mustapha)

Kasa
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Kasa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Next Post
Matatar Dangote Ta Ƙara Farashin Fetur, Ta Dakatar Da Lodi

Matatar Dangote Ta Ƙara Farashin Fetur, Ta Dakatar Da Lodi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.