Tsohon shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kebbi, Alhaji Muhammadu Besse, ya rasu a hannun ’yan bindiga bayan sace shi da suka yi.
An sace Besse ne a farkon wannan watan.
Wani ɗan jarida mai bibiyar harkokin tsaro a Arewa maso Yammacin Najeriya, Bakatsine ne, ya bayyana hakan a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X ranar Talata.
An yaɗa wani bidiyo inda aka ga Besse tare da wani mutum da aka sace suna shan wahala a hannun ’yan bindiga a dajin Birnin Gwari.
A cewar Bakatsine, Besse wanda shi ne tsohon shugaban APC na ƙaramar hukumar Koko/Besse, ya rasu kafin ya samu damar komawa wajen iyalansa.
Kawo yanzu shi da wanda aka gani a bidiyon da aka ɗauka a dajin Birnin Gwari duk sun rasa rayukansu yayin da suke tsare a hannun ’yan bindiga.
Bakatsine ya bayyana lamarin a matsayin babban abin takaici, yana mai cewa hakan ya sake nuna irin matsalolin tsaro da al’ummomin Arewacin Nijeriya ke fuskanta.
Ya kuma yi addu’ar Allah Ya gafarta musu, Ya sanya su a Aljannatul Firdausi, tare da bai wa iyalansu da masoyansu haƙurin jure wannan rashi.















Discussion about this post