ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ci Gaban Aikin Noma Na Sin Ke Samar Da Alfanu Ga Afirka

by Sulaiman
8 months ago

Kwanan nan, jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ta gudanar da babban taro kan ayyukan noma, inda aka tsara ayyukan raya ayyukan gona da kauyuka da kuma manoma cikin sabuwar shekara. A matsayinta na babbar kasa mai yawan mutane kimanin biliyan 1.4, gudanar da ayyukan noma da bunkasa ci gaban kauyuka da manoma daidai yadda ya kamata, da kuma samar da isashen abinci bisa karfin kanta, tushe ne na bunkasar kasar ta Sin, wanda hakan ke da matukar ma’ana wajen zamanantar da kasar.

Daga fuskantar talauci da rashin wadataccen abinci, zuwa samun isasshen abinci da kuma saurin ci gaban fasahar noma, Sin ba wai kawai ta dogara da kanta wajen biya bukatun jama’arta ta fannin abinci ba, har ma ta raba nasarorinta ga kasashe masu tasowa da ke ci gaba da fuskantar matsalolin rashin isashen abinci, musamman ma kasashen Afirka.

A cikin ‘yan shekarun nan, Sin da kasashen Afirka sun sami nasarori masu kyau bisa hadin gwiwarsu ta fannin aikin noma, har ma yawan cibiyoyin gwada fasahohin noma da Sin ta kafa a kasashen Afirka sun kai sama da 20, matakin da ya horar da dubban ma’aikatan fasahohin noma a wuraren.

ADVERTISEMENT

A kasashe kamar Burundi da Madagascar, shinkafar da aka inganta irinta da Sin ta kirkiro ta ba su damar girbin shinkafa da yawansa ya ninka sau 2 ko 3 bisa na lokacin da. A Rwanda da Mauritania, ana amfani da fasahar Juncao ta kasar Sin, wajen samar da harawa da noman laimar kwado, da kuma hana kwararowar hamada. A Kwadibuwa, tsarin sarrafa shinkafar da Sin ta bayar ya inganta wannan aiki bisa karuwar kashi 15%. Kuma ana taimaka wa Kenya da Madagascar wajen karfafa ingancin amfanin gona irinsu dangin gyada na Macadamia, da naman rago da sauransu, don su shiga kasuwar Sin.

Gogewa da dabarun ci gaban aikin noma na Sin tana amfanar da kasashen Afirka, kuma an yi imani cewa a nan gaba, kowane mataki na ci gaban aikin noma na Sin ba kawai zai kyauatata zaman rayuwar Sinawa ba, har ma zai taimaka wa kasashen Afirka su cimma burinsu na tsayawa da kafufuwansu wajen samun isasshen abinci, tare da zamanantar da aikin noma a kasashen.(Mai zane da rubutu: MINA)

LABARAI MASU NASABA

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwarzon Gwamnan Shekarar 2026 Kwamared Nasir Idris
  • Sulaiman
    Gwarzon Shekarar 2026 Abdulsamad Rabiu
  • Sulaiman
    Buƙatar Ɗaukar Matakan Daƙile Yaɗuwar Cutar Mashaƙo A Nijeriya
  • Sulaiman
    Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

MASU ALAKA

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Next Post

Kotu Ta Amince Da Aiwatar Da Sabbin Dokokin Haraji Daga 1 Ga Janairu

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki Na Ƙasa Gaba Ɗaya

September 11, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2026 Kwamared Nasir Idris

September 11, 2026

Dalilin Da Ya Sa Ba Zan Janye Wa Atiku Ba A Zaɓen 2027 – Peter Obi

September 11, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

Gwarzon Shekarar 2026 Abdulsamad Rabiu

September 11, 2026
Cutar Kwalara Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuƙe

Buƙatar Ɗaukar Matakan Daƙile Yaɗuwar Cutar Mashaƙo A Nijeriya

September 11, 2026
Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.