Mazauna unguwar Kawo a Jihar Kano na rayuwa cikin fargaba yayin da rikicin da ake zargin na ‘yan daba ne, ya shafe tsawon kwanaki uku a jere ana yin sa.
Rikicin ya kawo cikas ga harkokin yau da kullum, inda ’yan kasuwa da mutanen da ke wucewa a hanya suka ƙauracewa wajen saboda tsoro.
Yawancin mazauna yankin sun ce rikicin ya jefa kasuwancinsu cikin matsala tare da haifar da fargaba a yankin.
Mazauna unguwar sun ce rikicin ya fara ne kusan makonni uku da suka wuce bayan wata taƙaddama tsakanin ‘yan adaidaita sahu.
Daga baya rikicin ya rikiɗe zuwa ramuwar gayya tsakanin ɓangarori biyu.
Shaidu sun ce wani ɓangare na ‘yan daba ya tare hanya da sassafe, lamarin da ya haifar da tashin hankali, raunuka da lalata ababen hawa.
Tun daga lokacin, ɓangarorin biyu ke ci gaba da farmakar juna.
‘Yan unguwar sun bayyana halin da ake ciki a matsayin abin tsoro, inda suka ce yawan matasa masu ɗauke da makamai ya sanya zirga-zirgarsu cikin hatsari.
Wani ɗan gwagwarmaya a Kano ya dora laifin rikicin kan yawaitar shan miyagun ƙwayoyi da tasirin siyasa.
Ya kuma buƙaci shugabanni su ɗauki matakin gaggawa don daƙile matsalar faɗan daba.
Hukumomin tsaro sun ce suna sane da lamarin kuma suna aiki domin tabbatar da zaman lafiya.
Duk da bayanan da ’yansanda suka bayar, mazauna unguwar sun ce har yanzu suna cikin firgici, yayin da ba a tabbatar da adadin waɗanda suka jikkata ba.















Discussion about this post