‘Yan bindiga sun sace ƙanwar tsohon Ministan Wuta kuma mai neman takarar gwamnan Jihar Oyo a jam’iyyar APC, Bayo Adelabu, tare da tagwayen ‘ya’yanta.
Lamarin ya faru ne a ranar Laraba a yankin Challenge da ke birnin Ibadan, babban birnin jihar.
Wani daga cikin iyalan ya ce an kai farmaki ne a lokacin da iyalan ke fitowa daga gidansu da ke Elewura, Challenge, inda ‘yan bindigar suka tare su suka kuma tafi da su.
Mai magana da yawun Adelabu ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce matar da tagwayenta; Peter da Paul ne aka sace.
Wannan na zuwa ne a yayin da ake ci gaba da samun rahotannin sace-sacen mutane a Jihar Oyo.
A watan Mayu, an sace sama da malamai da ɗalibai 40 a wani hari a yankin Oriire, sannan a watan Disamban 2025, an kuma sace wani jigo na APC a Ibadan.
‘Yansanda sun ce har yanzu suna ƙoƙarin tantance bayanin abin da ya faru.















Discussion about this post