ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan ‘Yan Jarida 7 A Gombe 

by Sulaiman
5 months ago

Khalid Idris Doya

Wani mummunar hatsarin sakamakon fashewar tayar mota ya hallaka ‘yan jarida bakwai a kan hanyar Billiri zuwa Kumo da ke jihar Gombe a yayin da suke hanyarsu ta dawowa daga daurin auren abokiyar aikinsu a karamar hukumar Billiri da ke jihar a ranar Litinin.

Daga cikin wadanda suka rasa rayukansu har da ma’aikatan gidajen talabijin mallakin gwamnatin tarayya (NTA) da ke Gombe su 6 da wata ‘yar jarida guda daya lamarin da ya sanya jama’a cikin jimami.

  • Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Neman Belin Malami
  • Buƙatar A Sake Duba Sabuwar Dokar Haraji

Shugaban ‘yan jarida na kasa, (NUJ), Alhassan Yahya, ya bayyana matukar alhinisa kan wannan babban rashin da ‘yan jarida suka yi. Ya ce ranar ta zama ranar bakin ciki ga ‘yan jarida a jihar Gombe.

ADVERTISEMENT

Ma’aikatan NTA da suka rasa rayukansu a hatsarin sun hada da Manu Haruna Kwami, Manajan sashin mulki; Zarah Umar, Manhajar sashin labaru; Isa Edita a gidan talabijin din; Musa Tabra, tsohon manajan sashin labaru; Aminu, matukin motar da kuma Adams wanda ke kula da sashin Startimes na gidajen talabijin din.

Sai kuma dayan ‘yar jaridan da ita ma ta rasa rayuwarta a wannan hatsarin Misis Judith, wacce ma’aikaciya ce a ma’aikatar yada labarai ta jihar Gombe wacce ta ke aiki a hukumar samar da ilimi a matakin farko na jihar (SUBEB) a matsayin jam’iyar watsa labarai.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Bayan wadanda suka rasa rayukansu, akwai kuma sauran ‘yan jaridan da suka gamu da munanan raunuka da suka hada da Emmanuel Akila wakilin NTA a gidan gwamantin jihar, Nina da Jonathan Bara wadanda a halin yanzu suke kan amsar kulawar likitoci.

LEADERSHIP Hausa ta labaro cewa ko a ranar Juma’ar da ta gabata wasu ‘yan asalin kauyen Lawanti da ke karamar hukumar Akko ta jihar Gombe su bakwai (7) sun mutu a hatsarin mota a hanyarsu ta zuwa ɗaurin aure a jihar Borno. Wadanda hatsari a jeren sun jefa jama’an Gombe cikin tsaninin jimami da alhini.

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya samu mummunan labarin hatsarin da ya faru da ‘yan jarida, ma’aikatan Hukumar Gidan Talabijin na Najeriya (NTA) Gombe, da Ma’aikatan Yada Labarai cikin tsananin bakin ciki, firgici da juyayi.

A sanarwar da Kakakinsa Isma’ila Uba Misilli ya fitar, gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana hatsarin a matsayin wani mummunan lamari mai tayar da hankali wanda ya jefa Jihar Gombe cikin jimami, yana mai cewa rashin ya wuce na iyalai da hukumomi, ya ma taba ruhin kafofin watsa labarai da ma’aikata baki daya.

Gwamnan ya ce mamatan kwararru ne da suka sadaukar da rayuwarsu wajen fadakarwa, ilmantarwa da kuma yi wa jama’a hidima, yana mai bayyana mutuwarsu a matsayin mummunan koma-baya ga aikin jarida, da ayyukan gwamnati da kuma shugabanci a Jihar Gombe.

“Wannan ibtila’in abin tausayi ne kwarai. Mun rasa abokan aiki, abokan hulda a fagen ci gaba, kuma ma’aikatan gwamnati masu himma wadanda suka yi aiki tukuru da kuma jajircewa. Za mu dade muna jimamin wannan rashin a tsawon lokaci,” in ji Gwamnan.

Ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan, da shugabanni da membobin kungiyar ‘yan jarida ta Nijeriya, da shugabanni da ma’aikatan hukumar talabijin ta Nijeriya NTA da kuma dukkanin ‘yan jarida da ma’aikatan kafofin watsa labarai a ciki da wajen Jihar Gombe.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
  • Sulaiman
    Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
  • Sulaiman
    Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

MASU ALAKA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
Rahotonni

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati
Labarai

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare
Labarai

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

June 12, 2026
Next Post
Hukumar Hisbah Ta Kano Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama Da 12,000 A Shekarar 2025

Hukumar Hisbah Ta Kano Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama Da 12,000 A Shekarar 2025

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.