ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan ‘Yan Jarida 7 A Gombe 

by Sulaiman
6 months ago

Khalid Idris Doya

Wani mummunar hatsarin sakamakon fashewar tayar mota ya hallaka ‘yan jarida bakwai a kan hanyar Billiri zuwa Kumo da ke jihar Gombe a yayin da suke hanyarsu ta dawowa daga daurin auren abokiyar aikinsu a karamar hukumar Billiri da ke jihar a ranar Litinin.

Daga cikin wadanda suka rasa rayukansu har da ma’aikatan gidajen talabijin mallakin gwamnatin tarayya (NTA) da ke Gombe su 6 da wata ‘yar jarida guda daya lamarin da ya sanya jama’a cikin jimami.

  • Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Neman Belin Malami
  • Buƙatar A Sake Duba Sabuwar Dokar Haraji

Shugaban ‘yan jarida na kasa, (NUJ), Alhassan Yahya, ya bayyana matukar alhinisa kan wannan babban rashin da ‘yan jarida suka yi. Ya ce ranar ta zama ranar bakin ciki ga ‘yan jarida a jihar Gombe.

ADVERTISEMENT

Ma’aikatan NTA da suka rasa rayukansu a hatsarin sun hada da Manu Haruna Kwami, Manajan sashin mulki; Zarah Umar, Manhajar sashin labaru; Isa Edita a gidan talabijin din; Musa Tabra, tsohon manajan sashin labaru; Aminu, matukin motar da kuma Adams wanda ke kula da sashin Startimes na gidajen talabijin din.

Sai kuma dayan ‘yar jaridan da ita ma ta rasa rayuwarta a wannan hatsarin Misis Judith, wacce ma’aikaciya ce a ma’aikatar yada labarai ta jihar Gombe wacce ta ke aiki a hukumar samar da ilimi a matakin farko na jihar (SUBEB) a matsayin jam’iyar watsa labarai.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Bayan wadanda suka rasa rayukansu, akwai kuma sauran ‘yan jaridan da suka gamu da munanan raunuka da suka hada da Emmanuel Akila wakilin NTA a gidan gwamantin jihar, Nina da Jonathan Bara wadanda a halin yanzu suke kan amsar kulawar likitoci.

LEADERSHIP Hausa ta labaro cewa ko a ranar Juma’ar da ta gabata wasu ‘yan asalin kauyen Lawanti da ke karamar hukumar Akko ta jihar Gombe su bakwai (7) sun mutu a hatsarin mota a hanyarsu ta zuwa ɗaurin aure a jihar Borno. Wadanda hatsari a jeren sun jefa jama’an Gombe cikin tsaninin jimami da alhini.

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya samu mummunan labarin hatsarin da ya faru da ‘yan jarida, ma’aikatan Hukumar Gidan Talabijin na Najeriya (NTA) Gombe, da Ma’aikatan Yada Labarai cikin tsananin bakin ciki, firgici da juyayi.

A sanarwar da Kakakinsa Isma’ila Uba Misilli ya fitar, gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana hatsarin a matsayin wani mummunan lamari mai tayar da hankali wanda ya jefa Jihar Gombe cikin jimami, yana mai cewa rashin ya wuce na iyalai da hukumomi, ya ma taba ruhin kafofin watsa labarai da ma’aikata baki daya.

Gwamnan ya ce mamatan kwararru ne da suka sadaukar da rayuwarsu wajen fadakarwa, ilmantarwa da kuma yi wa jama’a hidima, yana mai bayyana mutuwarsu a matsayin mummunan koma-baya ga aikin jarida, da ayyukan gwamnati da kuma shugabanci a Jihar Gombe.

“Wannan ibtila’in abin tausayi ne kwarai. Mun rasa abokan aiki, abokan hulda a fagen ci gaba, kuma ma’aikatan gwamnati masu himma wadanda suka yi aiki tukuru da kuma jajircewa. Za mu dade muna jimamin wannan rashin a tsawon lokaci,” in ji Gwamnan.

Ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan, da shugabanni da membobin kungiyar ‘yan jarida ta Nijeriya, da shugabanni da ma’aikatan hukumar talabijin ta Nijeriya NTA da kuma dukkanin ‘yan jarida da ma’aikatan kafofin watsa labarai a ciki da wajen Jihar Gombe.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Hukumar Hisbah Ta Kano Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama Da 12,000 A Shekarar 2025

Hukumar Hisbah Ta Kano Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama Da 12,000 A Shekarar 2025

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.