ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar A Sake Duba Sabuwar Dokar Haraji

by Leadership Hausa
8 months ago

A makon da ya gabata ne, a shiga cikin wata zazzafar dambawar ka’addama kan zargin cushen a cikin dokokin harji na shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, wadda gwamnatinsa, ta gabatarwa da ‘yan majalisar kasar, ta kuma zamo doka.

Akasarin masu bibiyar lamarin, tun daga matakin farko na fara tsara kunkurin kafin ya zama doka.

Kundurin harajin sun zamo daka ne, biyo bayan faman tuntuba da aka ta hakilon yi, wanda kuma ake ta ci gaba da yin koarafi a kasar cewa, an dibga cushe a cikin dokokin na harajin, wadanda ‘yan majalisar suka amince da su.

ADVERTISEMENT

A yanzu haka dai, ana ganin akwai matukar bukatar a gudanar da cikakken bincike, kan batun zargin cushen da aka yi, a cikin dokikin harajin.

A watan Fabirairun 2025 ne, Majalisar Wakilai ta amince da dokokkin harin bayan gudanar da tarukan jin ra’ayoyin jama da kuma yin dubi kan wasu batun da za su iya janyo koma baya ga dokokin, wadanda daga baya, aka hade dokokin da sauran da Majalisar Dattawa, ta amince.

LABARAI MASU NASABA

Batun Shayar Da Jarirai Nonon Uwa Da Ƙalubalen Abinci Mai Gina Jiki

Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG

Dokokin guda hudu sun hada da, dokar haraji ta kasa da dokar haraji ta bangaren mulki da dokar haraji ta tara kudaden shiga da kuma dokar haraji ta hadaka ta hukumar tara haraji.

Shugaba Bola Tinubu ne, ya rattaba hannun kan wadannan dokokin a watan Yunin 2025, bisa nufin samar da sauye-sauye a tsarin tara haraji na kasa.

Sai dai, an tsara wadannan dokikin harajin, za su fara aiki ne gadan-gadana a watan Janairun 2026.

Amma sai wata takaddama ta kunno kai a tsakanin majalisar kasa bisa zargin da wasu ‘yan Majalisar Wakilai suka bijro da shin a cewa, an yin cushe, a cikin wadannan dokokin harajin tare da kuma wani zargin da wasu ‘yan kasar suka yi, na yin cushen.

Dan Majalisar Wakilai da ya fara bijiro da zargin cushen shi ne, Abdulsamad Dasuki, wanda ya sanar da cewa, dokokin harjin, sun saba da wadanda wanda ‘yan Majalisar suka amince da su, aka kuma gabatarwa da alummar kasa.

A cewarsa, wannan cushen ya sabawa kundin tsarin mulkin kasar nan da kuma dokokin kasar, kuma bai kamata Majalisar, ta yi sako-sako kan batun ba.

Sai dai, a martanin da Shugaban Majalisar Wakilai In response, Abbas Tajudeen, ya bayar da tabbacin cewa, Majalisar za ta dauki matakan da suka dace domin lalubo da mafita, kan batun.

Domin tabbatar da wannan alawashin na Abbas ne, ya sanya Majalisar ta kafa wani kwamiti na wucin gadi, mai mutane bakwai domin gudanar da bincike kan wannan batun na cushen.

Kwamtin a karkashin shugabancin dan Majalisa Aliyu Betara, ana sa ran zai kammala bincikensa ya kuma gabatar da rahoton sa a gaban Majalisar, nan da mako daya.

Wannan Jaridar na shawartar kwamitin da ya gudanar da aikinsa, ba tare da an yi masa, wani katsalandan ba kuma ba tare da sanya wata siyasa ba, ya kuma tabbatar da ya sanar da ‘yan Nijeriya binciken da ya gudanar.

Hakan ne, kawai zai sanya yakini da yarda, a cikin Zuciyoyin ‘yan kasar nan.

Kazalika, akwai matukar bukatar kwamtin ya gudanar da binciken sa, bisa ka’ida da kuma gaskiya.

Dole ne kuma bangaren zartarwa ya bari dokar kasa ta yi aikinta, yadda ya dace, musamman ba wai kawai domin zargin cushen ba, amma domin a kawar dukkan wani shakku daga cikin Zuciyar ‘yan kasar kan zargin batun na cushen.

Bugu da kari, abinda ya zarce batun kara samar da kudaden shiga da kuma kara tara harji ga kasar, doka za ta yi aikinta, wanda hakan zai kuma kara farkar da ‘yan Nijeriya, kan irin kudaden da Gwamnatin ke kashewa da tare da kuma tabbatar da tana bin ka’ida, wajen kashe kudaden.

Akwai bukatar a rinka tafiyar da komai yadda ya dace a kasar nan, duba da cewa, daukacin dokokin kasar, ba wai sune, suka kirkiri kansu da kansu ba.

Daukacin sabuntawar da za a yi domin tabbatar da inganci da kuma yin abinda ya dace, abu ne, da ba za a iya yin watsi, da hakan ba.

Dole ne dai, dokar ta faro daga wani wuri, wanda kuma aka tsar za fara fara wanzar da ita, gadan-gadan a ranar daya ga watan Janairun shekarar 2026.

A bisa ra’ayin mu, fara yin gwajin wadannan dokokin harjin a cikin kasa, zai tabbatar da saurin gudanar da garanbawul.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

Ra'ayinmu

Batun Shayar Da Jarirai Nonon Uwa Da Ƙalubalen Abinci Mai Gina Jiki

August 14, 2026
Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG
Ra'ayinmu

Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG

July 31, 2026
Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Next Post
Kudaden Paris Club: Ana Ce-ce-ku-ce Tsakanin Gwamnoni Da Ministan Shari’a

Kotu Ta Yi Watsi Da Bukatar Neman Belin Malami

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.