Wata bazawara, Misis Alheri Thomas, ta bayyana irin mummunan halin da ta shiga bayan da wasu ’yan bindiga suk kai hari ƙauyen Adama Dutse da ke ƙaramar hukumar Kajuru a Jihar Kaduna a ranar 18 ga watan Fabrairu, 2024.
Ta ce maharan sun shiga ƙauyen da misalin ƙarfe 6 na safe yayin da yawancin mazauna yankin ke barci.
“Sun shigo a hankali suka kewaye ƙauyen kafin su fara harbe-harbe,” in ji ta.
A cewarta, ’yan bindigar sun riƙa shiga gida-gida suna harbin mutane, yayin da wasu mazauna ƙauyen suka tsere zuwa daji domin tsira da rayukansu.
Misis Thomas ta ce ba ta gida lokacin da aka kai harin, lamarin da ya taimaka mata ta tsira da ranta.
Sai dai mijinta da ’ya’yanta huɗu suna cikin gida lokacin da maharan suka kai harin.
“Mijina da ’ya’yana huɗu suna cikin gida lokacin da ’yan bindigar suka kai hari. Dukkansu an kashe su,” in ji ta.
Ta kuma ce surukarta ta ga yadda aka kashe su, amma daga baya ita ma ta rasu sakamakon firgici da tashin hankalin da lamarin ya jawo mata.
Bayan kashe iyalinta, maharan sun ƙone gidansu tare da lalata dukiyoyinsu.
Misis Thomas ta bayyana harin a matsayin babban rashi da ya jefa ta cikin matsanancin damuwa da raɗaɗin zuciya.
Ta ƙara da cewa matsalar tsaro ta daɗe tana addabar yankin, amma ta ƙara tsananta a shekarar 2024, lamarin da ya sa mutane ke rayuwa cikin fargabar sake afkuwar hare-hare.















Discussion about this post