Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa hauhawar farashi da matsalar rashin tsaro na ci gaba da zama manyan ƙalubalen da ‘yan Nijeriya ke fama da su duk da sauye-sauyen tattalin arziƙi da tsaro da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ke aiwatarwa.
Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume ne, ya bayyana hakan a ranar Talata yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a Abuja domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya ta 2026.
Akume ya ce gwamnati na sane da wahalhalun da wasu manufofinta suka jawo wa jama’a, amma ya jaddada cewa an inganta tattalin arziƙin ƙasar.
Ya ce hauhawar farashi na ci gaba da jefa mutane cikin wahala, ko da yake a cewarsa tana raguwa a hankali.
Haka kuma, matsalar rashin tsaro na ci gaba da barazana ga rayuka da sana’o’in al’umma.
A cewarsa, tattalin arziƙin Nijeriya ya samu ci gaban kashi 4.07 cikin 100 a zangon ƙarshe na shekarar 2025, sannan ya ƙaru da kashi 3.89 cikin 100 a zangon farko na shekarar 2026.
Akume ya kuma bayyana cewa shirye-shiryen gwamnati kamar bayar da rance ga ɗalibai, tallafin kuɗi ga masu ƙaramin ƙarfi da kuma sauƙaƙa samun bashi sun taimaka wa mutane da dama.
Ya ce sama da ɗalibai miliyan ɗaya suka amfana da Asusun Ba da Lamunin Ilimi na Nijeriya (NELFUND), inda aka raba sama da Naira biliyan 184 domin biyan kuɗin makaranta da tallafin rayuwa.
Dangane da tsaro, Akume ya ce gwamnati na ƙara ɗaukar jami’an tsaro da samar musu da ƙarin kuɗaɗe, tare da haɗa kai da maƙwabtan ƙasashe da abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa wajen yaƙi da matsalolin tsaro.
Ya kuma buƙaci ‘yan Nijeriya su riƙa bai wa hukumomin tsaro bayanan sirri da suka dace, yana mai cewa tabbatar da tsaro nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa.
Sakataren ya kuma yi kira ga haɗin kan ƙasa, yana mai cewa ci gaba zai fi samuws idan jama’a suka fifita haɗin kai da amincewa da juna fiye da bambance-bambancen ƙabilanci da addini.
Ya ce gwamnati za ta ci gaba da aiwatar da sauye-sauyenta tare da neman goyon bayan ‘yan Nijeriya a zaɓen shekarar 2027 bisa sakamakon ayyukan da ta gudanar.
A nasa jawabin, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya ce Ranar Dimokuraɗiyya lokaci ne na girmama waɗanda suka yi gwagwarmayar tabbatar da mulkin dimokuraɗiyya.
Ya ƙara da cewa shekaru 27 ana mulkin dimokuraɗiyya ba tare da tsaiko ba babban abin alfahari ne a tarihin siyasar Nijeriya.














Discussion about this post