ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

by Sadiq
1 hour ago

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa hauhawar farashi da matsalar rashin tsaro na ci gaba da zama manyan ƙalubalen da ‘yan Nijeriya ke fama da su duk da sauye-sauyen tattalin arziƙi da tsaro da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ke aiwatarwa.

Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume ne, ya bayyana hakan a ranar Talata yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a Abuja domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya ta 2026.

Akume ya ce gwamnati na sane da wahalhalun da wasu manufofinta suka jawo wa jama’a, amma ya jaddada cewa an inganta tattalin arziƙin ƙasar.

ADVERTISEMENT

Ya ce hauhawar farashi na ci gaba da jefa mutane cikin wahala, ko da yake a cewarsa tana raguwa a hankali.

Haka kuma, matsalar rashin tsaro na ci gaba da barazana ga rayuka da sana’o’in al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Mijina Da ’Ya’yana 4 A Lokaci Ɗaya — Bazawara

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

A cewarsa, tattalin arziƙin Nijeriya ya samu ci gaban kashi 4.07 cikin 100 a zangon ƙarshe na shekarar 2025, sannan ya ƙaru da kashi 3.89 cikin 100 a zangon farko na shekarar 2026.

Akume ya kuma bayyana cewa shirye-shiryen gwamnati kamar bayar da rance ga ɗalibai, tallafin kuɗi ga masu ƙaramin ƙarfi da kuma sauƙaƙa samun bashi sun taimaka wa mutane da dama.

Ya ce sama da ɗalibai miliyan ɗaya suka amfana da Asusun Ba da Lamunin Ilimi na Nijeriya (NELFUND), inda aka raba sama da Naira biliyan 184 domin biyan kuɗin makaranta da tallafin rayuwa.

Dangane da tsaro, Akume ya ce gwamnati na ƙara ɗaukar jami’an tsaro da samar musu da ƙarin kuɗaɗe, tare da haɗa kai da maƙwabtan ƙasashe da abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa wajen yaƙi da matsalolin tsaro.

Ya kuma buƙaci ‘yan Nijeriya su riƙa bai wa hukumomin tsaro bayanan sirri da suka dace, yana mai cewa tabbatar da tsaro nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa.

Sakataren ya kuma yi kira ga haɗin kan ƙasa, yana mai cewa ci gaba zai fi samuws idan jama’a suka fifita haɗin kai da amincewa da juna fiye da bambance-bambancen ƙabilanci da addini.

Ya ce gwamnati za ta ci gaba da aiwatar da sauye-sauyenta tare da neman goyon bayan ‘yan Nijeriya a zaɓen shekarar 2027 bisa sakamakon ayyukan da ta gudanar.

A nasa jawabin, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya ce Ranar Dimokuraɗiyya lokaci ne na girmama waɗanda suka yi gwagwarmayar tabbatar da mulkin dimokuraɗiyya.

Ya ƙara da cewa shekaru 27 ana mulkin dimokuraɗiyya ba tare da tsaiko ba babban abin alfahari ne a tarihin siyasar Nijeriya.

MASU ALAKA

Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru
Manyan Labarai

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Mijina Da ’Ya’yana 4 A Lokaci Ɗaya — Bazawara

June 10, 2026
Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane
Manyan Labarai

Taɓarɓarewar Tsaro: Majalisar Wakilai Ta Gayyaci NSA da Ministoci Kan Yawaitar Satar Mutane

June 9, 2026
Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Shi Da Niyyar Ficewa Daga NDC – Kwankwasiyya

June 9, 2026

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

June 10, 2026
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Mijina Da ’Ya’yana 4 A Lokaci Ɗaya — Bazawara

June 10, 2026
Wang Yi Ya Bukaci A Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Wayewar Kai

Wang Yi Ya Bukaci A Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Wayewar Kai

June 9, 2026
ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
Bangaren Sin Ya Yi Kira Da a Dukufa Wajen Neman Mafita Ta Siyasa A Rikicin Ukraine

Bangaren Sin Ya Yi Kira Da a Dukufa Wajen Neman Mafita Ta Siyasa A Rikicin Ukraine

June 9, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’in Tsaro, Sun Yi Garkuwa Da Mutane Da Dama A Sokoto

June 9, 2026
Shugabannin Sin Da Koriya Ta Arewa Sun Sha Alwashin Wanzar Da Gagarumin Kawancen Gargajiya Tsakanin Kasashen Biyu

Shugabannin Sin Da Koriya Ta Arewa Sun Sha Alwashin Wanzar Da Gagarumin Kawancen Gargajiya Tsakanin Kasashen Biyu

June 9, 2026
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nemi A Haramta Shigo Da Yadiddika Domin Farfaɗo da Masaƙun Cikin Gida

June 9, 2026
Xi: An Cimma Matsayar Raya Dangantakar Sin Da Koriya ta Arewa A Sabon Zamani

Xi: An Cimma Matsayar Raya Dangantakar Sin Da Koriya ta Arewa A Sabon Zamani

June 9, 2026
Kwankwaso

A Shirye Nake In Sasanta Da Gwamnan Kano – Kwankwaso

June 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.