ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yakin Afghanistan Ba Fim Ba Ne

by CMG Hausa
4 years ago
Afghanistan

“Dana daya ya fado daga jirgin sama a filin jiragen sama na Kabul, dayan kuma har yanzu ba mu san inda yake ba”.

Kalaman da Mohammad Rezayee, dan kasar Afghanistan ya yi a kwanan baya a yayin da yake tattaunawa tare da jaridar The Times ta Burtaniya a kwanan baya, sun tunatar da mu kan abin da ya faru a shekara daya da ta gabata.

  • Nijeriya Da Amurka Sun Kulla Yarjejeniyar Dawo Da Kudaden Da Abacha Ya Wawure

A watan Agustan shekarar 2021, Amurka ta janye sojojinta daga kasar Afghanistan ba tare da daukar nauyin da ke bisa wuyanta ba, matakin da ya sa dubu dubantar ‘yan Afghanistan suka kutsa cikin filin jiragen sama na Kabul, inda jiragen saman dakon kaya na sojan Amurka suka tashi ba tare da yin la’akari da yadda ‘yan Afghanistan ke kokarin neman shiga jiragen, matakin da ya sa mutane da dama suka fado daga jirgin, kuma Zabi Rezayee mai shekaru 17 da haihuwa kuma dan Mohammad Rezayee, na daya daga cikin wadanda suka fado, a yayin da Zaki Rezayee, dansa na daban wanda a lokacin shi ma ya ke kan jirgin, amma an rasa inda yake.

ADVERTISEMENT

Yanzu iyalan Mohammad Rezayee na fuskantar kuncin rayuwa, sun sayar da kadarorinsu, kuma ba yadda za su yi su rufe shagon sai da ‘ya’yan itatuwa da ganyayen lambu da suka gudanar, duk da haka, wani lokaci ba su iya biya kudin burodi ba.

Abin da ya faru ga Mohammad Rezayee, yana kuma faruwa ga sauran ‘yan kasar ta Afghanistan.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Duk da cewa, a karshen watan Agustan bara, Amurka ta dasa aya ga yakin Afghanistan da ya tayar bisa sunan “yaki da ta’addanci”, amma ga mawuyacin halin da yakin ya haifar ga al’ummar kasar.

Baya ga haka, duk da cewa Amurka din ta janye sojojinta, amma tana ci gaba da kakaba wa kasar takunkumi, har ma ta haramta al’ummar kasar da ke fama da kunci yin amfani da kudadensu tare da neman satar wani kasonsu, lamarin da ya haifar da matsalar jin kai mai tsanani a kasar.

David Howell Petraeus, tsohon shugaban hukumar leken asiri ta kasar Amurka, ya taba amincewa da laifin da Amurka ta aikata cikin shekaru 20 da suka wuce a yayin da ta tura sojojin zuwa Afghanistan, kuma a yayin da ya tabo magana a kan yakin Afghanistan, ya kan ce, “ya yiwu ka gaji da kallon wani fim, kuma ka bar gidan sinima, a yayin da kuma fim din na ci gaba”.

Sai dai yakin Afghanistan ba fim ba ne. Yakin da Amurka ta kaddamar a Afghanistan cikin shekaru 20 da suka wuce, ya lalata kasar da kuma makomar al’ummar kasar, tare da halaka mutane dubu 174, ciki har da fararen hula sama da dubu 30, baya ga kuma miliyoyin al’ummar kasar suka zama ‘yan gudun hijira.

Lallai Amurka ta tafi bayan da ta gaji da yakin, amma da wuya a kawar da raunin da ya haifar ga al’ummar Afghanistan, wadanda yanzu haka miliyan 18.0 ke matukar fama da matsalar karancin abinci, kuma yara miliyan 3 sun kasa samun damar shiga makaranta.

Nan da wasu kwanaki, za a cika shekara guda da Amurka ta janye sojojinta daga Afghanistan.

Ya kamata gwamnatin Amurka ta yi na’am da laifukan da ta aikata, kuma ta dauki matakan da suka wajaba don biyan hasarorin da al’ummar Afghanistan suka sha.

Wani abu da ya fi muhimmanci kuma shi ne, bai kamata a manta da yakin Afghanistan ba, musamman ma kasar Amurka, dole ta yi koyi darasi daga yakin. (Mai zane:Mustapha Bulama)

Afghanistan
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Next Post
Yajin Aiki Zai Ci Gaba Tun Da Gwamnati Ta Kasa Dauki Matakin Da Ya Dace – ASUU

Yajin Aiki Zai Ci Gaba Tun Da Gwamnati Ta Kasa Dauki Matakin Da Ya Dace – ASUU

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.